Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe
Published: 10th, February 2025 GMT
Kotu ta tsare wani ɗan fashi da ya yi wa ɗalibai mata uku na Jami’ar Jihar Kwara fyaɗe.
Matashin da dubunsa ta cika yi wa ɗaliban fyade ne a yayin wani fashi a ɗakunan kwanan ɗalibai mata a cikin dare.
Ya yi musu wannan aika-aika tare da yunƙurin kisa ne a daƙinsu kwanan ɗalibai mata da ke wajen harabar jami’ar a yankin Malete a ranar 2 ga watan Disamba, 2024.
A yayin gurfanar da matashin a gaban Kotun Majiatare ta Jihar Kwara da ke birnin Ilorin, an tuhume shi da yin amfani da makami wajen yi wa ɗaliban munanan raunuka, tare da yi musu fyaɗe da kuma sace wayoyin iPhone 13 PronMax da iPhone 11 Pro Max.
’Yan sanda na neman ’yan bola-jari ruwa a jallo a Abuja 2027: Kwankwaso da Aregbesola sun gana kan makomar siyasar Najeriya“Kana gab da kashe ɗaya daga cikinsu ne aka kawo musu ɗauki, kuma bincike ya gano cewa kai ɗan ƙungiyar asiri ne tun shekarar 2020, kuma ƙungiyarku ta Aiye, ta yi ƙaurin suna wajen yin fashi da makami da aikata kisa da kuma yi wa ɗalibai mata fyaɗe,” kamar yadda ɗan sanda mai gabatar da ƙara, Nasiru Yusuf, ya karanta a takardar zargin matashin ɗan shekara 26.
Daga nan alƙalin kotun, Majistare Sa’idu ya ba da umarnin tsare wanda ake zargin tare da ɗage shari’ar zuwa ranar 20 ga watan nan na Fabrairu, 2025.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibai ɗalibai mata
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
Aƙalla masallata 40 ’yan bindiga suka sace a wani masallaci da ke Gidan Turbe a Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara da safiyar wannan Litinin.
Majiyoyi sun ce an yi awon gaba da masallatan ne zuwa dazukan Gohori da ke yankin Tsafe.
Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a LegasWannan harin dai kai tsaye masu ruwa da tsaki na kallonsa a matsayin kawo ƙarshen yarjejeniyar sulhu tsakanin ’yan bindigar da mahukuntan jihohin Zamfara da Katsina.
A baya-bayan nan ne jihohin Katsina da Zamfara suka ƙulla yarjejeniyar sulhu tsakaninsu da ’yan bindigar da suka addabi al’ummar jihohin arewa maso yammacin Najeriyar.
Yarjejeniyar sulhu da aka cimma a dajin Wurma ta samu halartan manyan ’yan bindiga irinsu Alhaji Usman Kachalla Ruga da Muhindinge da Yahaya Sani ( Hayyu ) da kuma Shu’aibu.
A ɓangaren mahukunta, akwai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi da kuma shugaban ƙaramar hukuma Babangida Abdullahi Kurfi.
’Yan bindiga sun saki wasu mutane da suke garkuwa da su a lokacin yarjejeniyar sulhun, tare da barin al’umma zuwa gonakinsu ba tare da wata fargaba ko tsangwama.
To sai dai kuma, ƙasa da wata guda bayan cimma wannan yarjejeniya, rahotanni sun ce ’yan bindiga sun kutsawa wani ƙauye a Zamfara tare da awon gaba da masallata.
Shaidun gani da ido sun ce, maharan sun yi wa masallacin ƙawanya da misalin ƙarfe 5:30 na safe, daidai lokacin da jama’a ke sallar asuba.