Aminiya:
2025-08-01@01:58:40 GMT

Ɗan sanda ya rataye kansa har lahira a Neja

Published: 9th, February 2025 GMT

Wani Mataimakin Sufeton ’Yan Sanda (ASP), Shafi’u Bawa, da ke aiki da Rundunar 61 Police Mobile Force a Kontagora da ke Jihar Neja, ya hallaka kansa har lahira.

Wani jami’in dan sanda ya shaida wa Aminiya cewa, lamarin ya faru ne a ranar Asabar.

Gwamnatin Kano ta dakatar da wani fim mai suna Zarmalulu Aisha Binani ce ta lashe zaɓen Adamawa, ina da ƙwararan hujjoji – Ari

An tsinci gawarsa rataye a cikin dakinsa.

Majiyoyi sun ce mahaifinsa, Malam Usman Bawa ne, ya fara gano abin da ya faru sannan ya kai rahoton lamarin zuwa ofishin ’yan sanda da ke Kontagora.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce: “A ranar 8 ga watan Fabrairu, 2025, da misalin karfe 2 na rana, an samu rahoton cewa ASP Shafi’u Bawa na Rundunar 61 PMF, Kontagora, ya rataye kansa.

“Har yanzu ba a san dalilin da ya sa ya aikata hakan ba.

“An dauke gawarsa tare da mika ta ga iyalansa domin yi mata jana’iza.

“Ana ci gaba da bincike don gano musabbabin faruwar lamarin.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rataye Kai

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta jihar Bauchi (BASIEC), Ahmed Makama Hardawa, ya rasu.

Marigayin ya rasu ne ranar Talata a Abuja, bayan ya yi fama da gajeruwar jinya.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed ne ya tabbatar da rasuwarsa a cikin wata sanarwa ranar Laraba.

Muna tafe da karin bayani…

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa
  • Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata