Aminiya:
2025-11-02@03:47:12 GMT

’Yan bindiga sun mamaye masallaci sun yi awon gaba da masallata a Sakkwato

Published: 7th, February 2025 GMT

Wasu da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne sun yi garkuwa da wasu masallata a wani masallaci a unguwar Bushe da ke Ƙaramar hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato.

Waɗanda da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai farmaki masallacin ne da asubahin ranar Alhamis a yayin da masu ibada ke yin Sallar Subhi da asuba.

Lakurawa sun kashe mutum 1 sun jikkata 6 a Kebbi Yadda bom din Boko Haram ya kashe mutane a hanyar kasuwa a Adamawa

Aƙalla masallata 10 da suka haɗa da Limamin ne aka ce an yi awan gaba da su a yayin harin.

Jaridar Punch ta ruwaito DSP Ahmed Rufa’i, kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Sakkwato ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Juma’a.

Rufa’i ya ce, rundunar ’yan sandan tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro, suna aiki tuƙuru don ganin an sako dukkan waɗanda lamarin ya shafa cikin gaggawa.

Ya ce: “Na tabbatar da faruwar lamarin ne daga bakin babban jami’in ofishin ’yan sanda DPO na unguwar lokacin da na zanta da shi ta wayar tarho.

“Ina so in tabbatar muku cewa, rundunar ’yan sandan Nijeriya tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro suna aiki tuƙuru don ganin an sako dukkan waɗanda aka yi garkuwa cikin gaggawa.”

Shima Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Sakkwato mai wakiltar yankin Sa’idu Ibrahim ya tabbatar da faruwar lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sakkwato yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi

’Yan bindiga sun sace Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Honarabul Samaila Bagudu, a garinsu da ke Ƙaramar Hukumar Bagudu.

Rahotanni sun bayyana cewa ’yan bindigar sun mamaye garin Bagudu ne da yammacin ranar Juma’a tare da yin harbe-harbe don tsorata al’umma.

Maharan sun yi awon gaba da ɗan majalisar ne a kan hanyarsa ta dawowa daga masallaci bayan ya an idar da sallah masallaci a garin na Bagudu.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnatin Jihar Kebbi, Ahmed Idris, ya ce an sanar da hukumomin tsaro, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da kuɓutar da Mataimakin Shugaban Majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja