Aminiya:
2025-09-17@22:08:03 GMT

’Yan bindiga sun mamaye masallaci sun yi awon gaba da masallata a Sakkwato

Published: 7th, February 2025 GMT

Wasu da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne sun yi garkuwa da wasu masallata a wani masallaci a unguwar Bushe da ke Ƙaramar hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato.

Waɗanda da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai farmaki masallacin ne da asubahin ranar Alhamis a yayin da masu ibada ke yin Sallar Subhi da asuba.

Lakurawa sun kashe mutum 1 sun jikkata 6 a Kebbi Yadda bom din Boko Haram ya kashe mutane a hanyar kasuwa a Adamawa

Aƙalla masallata 10 da suka haɗa da Limamin ne aka ce an yi awan gaba da su a yayin harin.

Jaridar Punch ta ruwaito DSP Ahmed Rufa’i, kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Sakkwato ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Juma’a.

Rufa’i ya ce, rundunar ’yan sandan tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro, suna aiki tuƙuru don ganin an sako dukkan waɗanda lamarin ya shafa cikin gaggawa.

Ya ce: “Na tabbatar da faruwar lamarin ne daga bakin babban jami’in ofishin ’yan sanda DPO na unguwar lokacin da na zanta da shi ta wayar tarho.

“Ina so in tabbatar muku cewa, rundunar ’yan sandan Nijeriya tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro suna aiki tuƙuru don ganin an sako dukkan waɗanda aka yi garkuwa cikin gaggawa.”

Shima Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Sakkwato mai wakiltar yankin Sa’idu Ibrahim ya tabbatar da faruwar lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sakkwato yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

An garzaya da shi zuwa babban Asibitin Gwamnatin Tarayya da ke Birnin Kebbi, inda daga bisani likitoci suka tabbatar da rasuwarsa.

An yi jana’izarsa a babban masallacin Sarkin Gwandu, sannan aka binne shi a makabartar Dukku da ke kan hanyar Makera zuwa Kangiwa.

Jana’izar ta samu halartar jami’an kwas5tan, ‘yan uwa, abokai da sauran mu5sulmi daga sassa daban-daban na jihar.

Har yanzu al’ummar garin Filgila da kewaye na cikin tashin hankali da fargaba, kasancewar hare-haren Lakurawa na jefa su cikin zulumi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin