Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kara kudirin kasafin kudin shekarar 2025 daga naira tiriliyan 49.7 zuwa naira tiriliyan 54.2, yayin da majalisar dokokin kasar ke kokarin ganin an zartar da shi kafin karshen wata.

Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya sanar da karin kasafin ta hanyar wasiku daban-daban da shugaba Tinubu ya aikewa majalisar dattawa da ta wakilai.

A cikin wasikar da aka karanta yayin zaman majalisar, Sanata Godswill Akpabio ya ce an sami  karin kudin ne sakamakon karin kudaden shigar da hukumar tara haraji ta kasa FIRS ta samu na Naira tiriliyan 1.4, yayin da hukumar hana fasakwabri  ta kasa ta tara Naira tiriliyan 1.2, da kuma Naira tiriliyan 1.8 da wasu hukumomin gwamnati suka tara.

A don haka shugaban majalisar ya mika bukatar ga kwamitin kasafin kudi na majalisar dattawa domin tantancewa cikin gaggawa, inda ya tabbatar da cewa za a kammala nazarin kasafin kudin kafin karshen wata.

Daga Bashir Meyere

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Naira tiriliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Tarayyar Turai Ta Yi Barazanar Karin Matsin Lamba Akan “Isra’ila”

Wasu jami’an diplomasiyyar turai sun yi wa gwamnatin Benjamin Netanyahu da cewa za ta fuskanci Karin matsin lamba idan har ba ta sauya halayyarta akan Gaza ba.

Jaridar “Washington Post” ta Amurka ta ambato jami’an diplomasiyyar turai suna cewa; sabon tsarin da ake yin aiki da shi na raba kayan agaji a Gaza, ya juya ya zama harigitsi kuma ana bude wuta akan mutane da hakan ya yi sanadiyyar jikkatar Falasdinawa da dama.”

Har ila yau jami’an diplomasiyyar na turai sun ce, ko kadan ba su da aniyar bayar da kayan agajinsu ga masu tafiyar da tsarin da su ne Isra’ila da Amurka.”

 Bugu da kari, majiyar diplomasiyyar ta tarayyar turai ta ci gaba da cewa; Hotunan masu ban tsoro da suke fitowa daga Gaza, sun kai musu iya wuya, ba za su iya ci gaba da jurewa ganinsu ba.”

A cikin kwanakin bayan nan dai kasashen turai sun fara yin matsin lamba akan HKI da ta bari a shigar da kayan agaji cikin yankin na Gaza da kuma yadda take ci gaba da kashe fararen hula da kuma rusau din da take yi mai yawa.

A karon farko, tun kirkirar HKI, kasar Jamus ta soki siyasar Tel Avi akan Gaza, da hakan yake nuni da yadda kasashen turai din suke kara matsin lamba.

Shugaban gwamnatin jamus  Friedrich Merz ya ce; Harin da Isra’ila ta kai wa wata makaranta a Gaza, ya tashi daga karkashin fada da ta’addanci, ya zama wani abu daban.”

A can kasar ta jamus din dai jam’iyyar hamayya ta ” Green Party” ta ce; bai kamata a rika amfani da makaman kasar Jamus a yakin Gaza ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Taron Kungiyar BRICS Zai Kawo Bunkasar Tattalin Arziki
  • Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
  • ‘Yan Wasan Kano Sun Rasu Sanadiyar Hadarin Mota Yayin Dawowa Daga Gasar Wasanni Ta Kasa
  • Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
  • Hana shigar da abinci da Isra’ila ta yi zuwa Gaza ‘laifi ne na yaki’: MDD
  • Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu
  • Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta
  • Tarayyar Turai Ta Yi Barazanar Karin Matsin Lamba Akan “Isra’ila”
  • Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana
  • Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa