Aminiya:
2025-08-01@13:50:42 GMT

Hausawa sun yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri

Published: 5th, February 2025 GMT

A kwanakin baya Hausawa mazauna Jahar Imo suka yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri Fadar Gwamnatin Jihar Imo da ke yankin Kudu maso Gabas yankin da ake kira da Ibo.

Hausawa mazauna Jihar Imo da ke Owerri babban birnin jahar a kwanan baya sun yi bikin cika shekara 153 da zuwa Owerri, Jahar Imo da zama domin gudanar da harkokin na kasuwanci.

DAGA LARABA: Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma ‘Event Centre’ Sarki Sanusi ya ziyarci unguwar da mutane suka rasu a dalilin rusau

Yawancin garurukan Asaba da Benin da Obudu a Jihar Kuros Riba su ne mazaunin Hausawa na farko a Jahar Kuros Riba sai kuma garin Alele a Jihar Ribas mai iyaka da Jihar Bayelsa da garin Fatakwal da sauran wasu garuruka a Kudu maso Kudu da garin Anaca Jahar Anambra.

Hausawa sun zo garin Owerri tun kimanin shekara 153, wanda akasarinsu Kanawa ne daga garin Tsakuwa da ke Ƙaramar Hukumar Garko da ke Jihar Kano, kamar yadda Sarkin Hausawan Owerri, Alhaji Auwalu Baba Sai’idu Sulaiman ya shaida wa Aminiya.

Masarautar Hausawan kamar yadda Sarkin Alhaji Sai’du Suleiman ya tabbar, tana ƙunshe da ƙabilun Arewacin Nijeriya Musulmi da waɗanda ba Musulmai, suna zaune lafiya tsakaninsu da kuma ’yan asalin jihar.

Ko a gwamnatin da ta shude tsohon Gwamnan Jihar Imo ya naɗa ɗan Arewa muƙamin mataimaki na musamman kan harkokin baki wadanda ba ’yan asalin jihar ba.

Ta bangaren ci gaba da bmazauna Jahar Imo da kuma babban birnin Owerri, Sarkin ya ci gaba da cewa, “Wannan masarauta tana da hakimi guda da dagaci guda da ke kowace karamar hukuma da ke Jihar Imo guda 27 da ke daukacin kananan hukumomin 27 na Jihar ke nan.”

Da yake karin haske game da masarautar, kakakin Sarkin, Nura Bala Ajingi ya ce, masarauta ta faɗaɗa ne zuwa sauran kananan hukumomin da aka ambata saboda ci gaban da ake samu na al’ummar Arewa mazauna jahar a karkashin wannan masarauta da Alhaji Auwal Baba Sa’idu ke shugabanta.

Haka nan kuma sarkin Hausawa Owerri shi ne sakataren sarakunan daukacin majalisar sarakunan Hausawa mazauna shiyyar Kudu maso Gabashin Nijeriya.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hausawa Jihar Imo Jihar Kano shekara 153

এছাড়াও পড়ুন:

Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka

Ministan kasuwanci na Afirka ta Kudu Parks Tau ya fada jiya Alhamis cewa kasarsa na shirin yin shawarwarin kasuwanci da nufin kaucewa harajin kashi 30% na Amurka a kan kasarsa, wanda  zai fara aiki daga wannan Juma’a.

A farkon watan Mayu ne Afirka ta Kudu ta gabatar da wani shirin  yarjejeniya ta kasuwanci ga gwamnatin Trump, amma kuma gwamnatin Amurka bat a bayar da amsa kan hakan ba.

kuma ta sake duba ta a watan Yuni, ba tare da bayar da amsa ba.

Ya kara da cewa, jami’an  Afirka ta Kudu sun yi magana da jami’an Amurka a yammacin Laraba a ofishin jakadancin Washington da ke Pretoria da kuma wakilin kasuwanci na Amurka, amma har yanzu akwai rashin tabbas game da abin da zai faru yayin da wa’adin haraji yake karewa.”

Ya kara da cewa, “Sun ce za su kara mana kwarin gwiwar sake mika kudirinmu, mai yiyuwa ya karfafa gwamnatin Amurka ta sake yin nazari kan batun haraji.”

Amurka ita ce kasa ta biyu wajen cinikayya da kasar  Afirka ta Kudu bayan kasar Sin. Afirka ta Kudu na fitar da motoci, wasu kayayyaki da aka kerawa, ‘ya’yan itatuwa, da inabi zuwa Amurka.

Dangantaka tsakanin kasashen biyu ta yi tsami ne kan manufofin karfafa tattalin arziki ga bakaken fata ‘yan Afirka ta Kudu, da nufin magance matsalar rashin daidaito da aka yi a shekaru aru-aru, da kuma batun karar da Afirka ta kudu ta shigar kan kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli August 1, 2025 Gaza: Mutane Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Wasu Kuma Sun Jikkata August 1, 2025 Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan August 1, 2025 Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar August 1, 2025 Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya August 1, 2025 Sayyid Abdulmalik Husi: Taimakon Da Ake Jefawa Gaza Ta Sama Yaudara Ce August 1, 2025 Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka July 31, 2025 Ministan Harkokin Wajen Siriya Yana Rasha Don Bude Sabon Shafi Tsakaninsu July 31, 2025 Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara July 31, 2025 Canada Zata Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu A Taron MDD July 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
  • Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka
  • Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu
  • Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • ’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau