Hausawa sun yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri
Published: 5th, February 2025 GMT
A kwanakin baya Hausawa mazauna Jahar Imo suka yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri Fadar Gwamnatin Jihar Imo da ke yankin Kudu maso Gabas yankin da ake kira da Ibo.
Hausawa mazauna Jihar Imo da ke Owerri babban birnin jahar a kwanan baya sun yi bikin cika shekara 153 da zuwa Owerri, Jahar Imo da zama domin gudanar da harkokin na kasuwanci.
Yawancin garurukan Asaba da Benin da Obudu a Jihar Kuros Riba su ne mazaunin Hausawa na farko a Jahar Kuros Riba sai kuma garin Alele a Jihar Ribas mai iyaka da Jihar Bayelsa da garin Fatakwal da sauran wasu garuruka a Kudu maso Kudu da garin Anaca Jahar Anambra.
Hausawa sun zo garin Owerri tun kimanin shekara 153, wanda akasarinsu Kanawa ne daga garin Tsakuwa da ke Ƙaramar Hukumar Garko da ke Jihar Kano, kamar yadda Sarkin Hausawan Owerri, Alhaji Auwalu Baba Sai’idu Sulaiman ya shaida wa Aminiya.
Masarautar Hausawan kamar yadda Sarkin Alhaji Sai’du Suleiman ya tabbar, tana ƙunshe da ƙabilun Arewacin Nijeriya Musulmi da waɗanda ba Musulmai, suna zaune lafiya tsakaninsu da kuma ’yan asalin jihar.
Ko a gwamnatin da ta shude tsohon Gwamnan Jihar Imo ya naɗa ɗan Arewa muƙamin mataimaki na musamman kan harkokin baki wadanda ba ’yan asalin jihar ba.
Ta bangaren ci gaba da bmazauna Jahar Imo da kuma babban birnin Owerri, Sarkin ya ci gaba da cewa, “Wannan masarauta tana da hakimi guda da dagaci guda da ke kowace karamar hukuma da ke Jihar Imo guda 27 da ke daukacin kananan hukumomin 27 na Jihar ke nan.”
Da yake karin haske game da masarautar, kakakin Sarkin, Nura Bala Ajingi ya ce, masarauta ta faɗaɗa ne zuwa sauran kananan hukumomin da aka ambata saboda ci gaban da ake samu na al’ummar Arewa mazauna jahar a karkashin wannan masarauta da Alhaji Auwal Baba Sa’idu ke shugabanta.
Haka nan kuma sarkin Hausawa Owerri shi ne sakataren sarakunan daukacin majalisar sarakunan Hausawa mazauna shiyyar Kudu maso Gabashin Nijeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hausawa Jihar Imo Jihar Kano shekara 153
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
Hukumar Jin Daɗin Alhazai a Jihar Kebbi ta bayyana cewa ta kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin bana a Ƙasa Mai Tsarki.
Amirul Hajji na jihar na shekarar 2025 kuma Sarkin Argungu, Alhaji Samaila Muhammad Mera, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a lokacin taron farko da aka gudanar a hedkwatar hukumar da ke Birnin Kebbi.
Ya kuma yi alkawarin tabbatar da jin daɗin mahajjatan jihar yayin da suke a ƙasa mai tsarki.
Amirul Hajjin ya bayyana cewa jimillar mahajjata 3,800 daga jihar ne suka biya kuɗin kujerunsu gaba ɗaya domin aikin hajjin bana, kuma jigilar mahajjatan za ta fara ne ranar 9 ga watan Mayu, inda ya ce da yardar Allah za a ci gaba da jigilar ba tare wani tsaiko ba har sai an kammala.
Ya kuma bayyana cewa, a wannan shekarar, za a yi wa mahajjata canjin kuɗin guzirinsu na BTA zuwa kudin Saudiyya wato riyal kai tsaye, da nufin dakile ayyukan damfara da kuma kare mahajjata daga asarar kuɗi yayin musayar kuɗaɗe a nan gida da kuma Saudiyya.
Alhaji Muhammadu Mera ya shawarci mambobin tawagar gwamnati da jami’an hukumar jin daɗin mahajjata da su gudanar da ayyukansu bisa tsoron Allah, tare da kare haƙƙoƙin mahajjata, daidai da manufar Gwamna Nasir Idris na gudanar da sahihin aikin Hajji mafi kyau.
Shugaban Hukumar, Alhaji Faruk Musa Yaro, ya yi alkawarin bayar da cikakken haɗin kakaga tawagar gwamnati domin tabbatar da nasarar aikin Hajji da ba a taɓa irin sa ba a tarihin jihar.
Ya ce an riga an samu masauki da sauran abubuwan buƙata ciki har da sufuri da abinci a ƙasa mai tsarki, sannan kuma kamfanin jirgin samsada ya yi jigilar Alhazan jihar a shekarar da ta gabata, wato Flynas, a bana ma shi ne zau yi jigilar mahajjatan zuwa kasa mai tsarki.
Haka kuma, an an fara yi wa Amirul Hajj da sauran mambobin tawagar gwamnati allurar rigakafi yayin kaddamar da shirin rigakafin mahajjatan.
Daga Abdullahi Tukur