Aminiya:
2025-09-18@02:18:13 GMT

Hausawa sun yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri

Published: 5th, February 2025 GMT

A kwanakin baya Hausawa mazauna Jahar Imo suka yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri Fadar Gwamnatin Jihar Imo da ke yankin Kudu maso Gabas yankin da ake kira da Ibo.

Hausawa mazauna Jihar Imo da ke Owerri babban birnin jahar a kwanan baya sun yi bikin cika shekara 153 da zuwa Owerri, Jahar Imo da zama domin gudanar da harkokin na kasuwanci.

DAGA LARABA: Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma ‘Event Centre’ Sarki Sanusi ya ziyarci unguwar da mutane suka rasu a dalilin rusau

Yawancin garurukan Asaba da Benin da Obudu a Jihar Kuros Riba su ne mazaunin Hausawa na farko a Jahar Kuros Riba sai kuma garin Alele a Jihar Ribas mai iyaka da Jihar Bayelsa da garin Fatakwal da sauran wasu garuruka a Kudu maso Kudu da garin Anaca Jahar Anambra.

Hausawa sun zo garin Owerri tun kimanin shekara 153, wanda akasarinsu Kanawa ne daga garin Tsakuwa da ke Ƙaramar Hukumar Garko da ke Jihar Kano, kamar yadda Sarkin Hausawan Owerri, Alhaji Auwalu Baba Sai’idu Sulaiman ya shaida wa Aminiya.

Masarautar Hausawan kamar yadda Sarkin Alhaji Sai’du Suleiman ya tabbar, tana ƙunshe da ƙabilun Arewacin Nijeriya Musulmi da waɗanda ba Musulmai, suna zaune lafiya tsakaninsu da kuma ’yan asalin jihar.

Ko a gwamnatin da ta shude tsohon Gwamnan Jihar Imo ya naɗa ɗan Arewa muƙamin mataimaki na musamman kan harkokin baki wadanda ba ’yan asalin jihar ba.

Ta bangaren ci gaba da bmazauna Jahar Imo da kuma babban birnin Owerri, Sarkin ya ci gaba da cewa, “Wannan masarauta tana da hakimi guda da dagaci guda da ke kowace karamar hukuma da ke Jihar Imo guda 27 da ke daukacin kananan hukumomin 27 na Jihar ke nan.”

Da yake karin haske game da masarautar, kakakin Sarkin, Nura Bala Ajingi ya ce, masarauta ta faɗaɗa ne zuwa sauran kananan hukumomin da aka ambata saboda ci gaban da ake samu na al’ummar Arewa mazauna jahar a karkashin wannan masarauta da Alhaji Auwal Baba Sa’idu ke shugabanta.

Haka nan kuma sarkin Hausawa Owerri shi ne sakataren sarakunan daukacin majalisar sarakunan Hausawa mazauna shiyyar Kudu maso Gabashin Nijeriya.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hausawa Jihar Imo Jihar Kano shekara 153

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha

Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan wanda yake halartar taron brinin Doha, na kasashen musulmi da larabawa, ya gaba da sarkin Qatar Tamim Bin Hamad ali-Thani, inda su ka tattaunawa halin da ake ciki a wannan yankin na yammacin Asiya.

Taron na Doha ne na gaggawa ne wanda aka shriya shi, domin tattauna harin wuce gona da iri da HKI ta kai wa kasar Qatar a wani yunkurin yi wa shugabannin Falasdinawa kisan gilla.

A yayin wancan harin dai, ‘yan sahayoniyar sun harba makamai masu linzami fiye da 10 akan wani gini wanda jami’an kungiyar gwgawarmayar musulunci ta Hamas suke taro a ciki.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka  Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan:  Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato