An shawarci gwamnonin jihohin Arewa da su yi koyi da gwamnatin jihar Neja wajen magance matsalolin rikicin makiyaya da manoma a yankin domin samun ci gaba mai dorewa.

Shugaban kungiyar Miyetti Allah ta kasa MACBAN, Dokta Baba Usman Ngelzarman ne ya bayar da wannan shawarar a wajen wani taro na musamman na karramawa  tare da tabbatar da lakabin gargajiya ga wasu fitattun Fulani guda biyu a jihar Neja, da aka gudanar a fadar Sarkin Minna.

Dokta Baba Usman Ngelzarman ya bayyana cewa, hanyar da Gwamna Mohammed Umar Bago na Jihar Neja ya bi na samar da sakamako mai kyau, ta yadda za a rage yawan rikicin makiyaya da manoma a jihar abin a yaba ne matuka.

A cewarsa hakan ya sanya bangarorin 2 sun kara fahimta da mutunta juna, wanda ya haifar da karuwar kudaden shiga a jihar da ma Najeriya baki daya.

Mai martaba Sarkin Minna Dr Umar Faruk Bahago, ya jaddada bukatar masu rike da mukaman gargajiya a yankinsa su rika gudanar da ayyukansu bisa tsoron Allah,  ta hanyar yin adalci ga kowa, don samun nasara.

A nasa jawabin sabon Jauro Minna kuma Kwamishinan kula da harkokin Makiyaya da kiwo na jihar Neja, Umar Ahmed Rebe ya yi alkawarin kara himma wajen inganta alakar manoma da makiyaya, wadda  za ta ci gaba da  kasancewa cikin kwanciyar hankali da walwala domin samun kyakkyawan sakamako.

A nashi jawabin, Wakilin Fulanin Minna, Alhaji Hassan Usman Shiroro, ya yi kira ga Fulanin jihar Neja da su ci gaba da zama lafiya da kowa domin bunkasa ci gaban jihar Neja cikin hanzari, yana mai jaddada cewa zaman lafiya shi ne abin da ake bukata na duk wani ci gaba mai ma’ana.

Daga Aliyu Lawal

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jihar Neja Kungiyar Miyetti Allah

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

Rundunar sojin ba ta fitar da sanarwa ba game da wannan hari na baya-bayan nan, amma hukumar DSS ta tabbatar da faruwar lamarin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Gwamnatin Kano Ta Kammala Gyaran Makarantu Sama Da 1,200 A Kananan Hukumomi 44
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa