HausaTv:
2025-09-17@23:28:29 GMT

Rahoto : Amurka Na Matsin Lamba Wa Ukraine Ta Gudanar Da Zabe Zuwa Karshen Shekara

Published: 2nd, February 2025 GMT

Rahotanni sun ce gwamnatin shugaban Amurka Donald Trump na matsawa kasar Ukraine lamba domin gudanar da zabuka a karshen wannan shekara a daidai lokacin da ake kokarin kulla yarjejeniyar sulhu tsakanin Kiev da Moscow.

Wakilin Trump na musamman kan Ukraine da Rasha, Keith Kellogg, ya fada a wata hira da ya yi da kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin Ukraine da aka dakatar a yakin da ake yi da Rasha, suna bukatar a gduanar da su.

“Yawancin kasashen dimokuradiyya suna gudanar da zabe a lokacin yakinsu. Ina ganin yana da mahimmanci su yi haka,”in ji Kellogg.

Kamfanin dillancin labaran reuters ma ya rawaito wasu jami’an fadar White House sun tattauna batun matsawa Ukraine ta amince da gudanar da zabe a wani bangare na duk wata yarjejeniya ta farko da Rasha.

Trump da Kellogg sun ce suna aiki kan wani shiri na shiga tsakani a cikin watannin farko na sabuwar gwamnatin Amurka don kawo karshen yakin da ya barke a watan Fabrairun 2022.

Har yanzu dai ba a fayyace shirin ba kuma har yanzu ba a san yadda za a karbi shirin a cikin kasar Ukraine domin kawo karshen rikicin mafi muni a Turai tun bayan yakin duniya na biyu.

A baya shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskyy ya ce Kiev za ta iya gudanar da zabe a wannan shekara idan fadan ya kare da kuma samar da kwakkwaran tabbacin tsaro ga Ukraine.

A cikin shekarar 2024 ne wa’adin shekaru biyar na Zelensky ya kamata ya kare amma ba’a iya gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisa a karkashin dokar soja ba, wanda Ukraine ta sanya a watan Fabrairun 2022.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta ce Najeriya na rasa sama da Dala Biliyan 10 duk shekara sakamakon asarar amfanin gona bayan girbi.

Ministan Noma  Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a wajen kaddamar da shirin Hanyar Inganta Noma da Kayayyakin Mire Rayuwa a Yankunan Karkara G.R.A.I.N a ƙaramar hukumar Birnin Kudu ta  Jihar Jigawa.

 

Ya ce asarar na faruwa ne saboda rashin ingantattun wuraren ajiya, karancin ababen more rayuwa, sauyin yanayi da kuma ambaliya.

Kyari ya bayyana cewa noma na bada gudunmawar kashi 24 bisa 100 na Jimillar Darajar Kayayyaki da Ayyuka da Kasa ta Samar a Cikin Shekara GDP, inda ƙananan manoma ke samar da sama da kashi 70 bisa 100 na abincin da ake ci a ƙasa.

Ya jaddada cewa gwamnati za ta tallafa musu da kayan noma na  zamani da wuraran kasuwanci domin inganta tattalin arziki.

A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi na Jigawa ya yaba da samun Cibiyar Cigaban Karakara ta Pulse ta farko a Jigawa, yana mai cewa za ta kawo sauyi a harkar noma da rayuwar jama’ar karkara.

Haka zalika, shi ma Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu zai taimaka wajen ci gaban tattalin arziki.

Shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kudu, Alhaji Builder Muhammad Uba, ya jaddada goyon bayansa ga shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Tinubu tare da yabawa gwamnatin Namadi kan sauya fasalin noma a jihar.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Bida Poly ta kawo sojoji su kula da jarrabawar ɗalibai
  • Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”