Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ya Raba Sama Da Miliyan 75 Ga Marasa Galihu
Published: 2nd, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta ce za a ci gaba da bada tallafi ga al’umma a dukkan mazabu 30 na ‘yan majalisar dokokin Jihar.
Gwamnan Jihar Malam Umar Namadi ya bada wannan tabbacin a lokacin da yake kaddamar da bada tallafi ga al’ummar karamar hukumar Miga wanda Shugaban majalisar dokokin Jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya raba fiye da Naira Miliyan 75 ga masu karamin karfi.
Malam Umar Namadi, ya yaba da tsarin bada tallafin ga al’ummar karamar hukumar ta Miga.
A cewarsa, tsarin bada wannan tallafi da kakakin majalisar ya yi ya dace da kudirorin gwamnatin jihar 12.
Yana mai nuni da cewar, a kowacce Karamar Hukuma za a kaddamar da irin wannan tallafi domin bunkasa tattalin arzikin al’umma don su zamo masu dogaro da kai.
Namadi, ya ce bullo da tsarin bada tallafin ya nuna cewar ‘yan majalisar Jihar suna tare da al’ummarsu.
Shi kuwa a nasa jawabin, Kakakin majalisar dokokin jihar Jigawan Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya ce rabon tallafin ya tasamma fiye da Naira Miliyan 75 wanda al’ummar mazabar Miga ne za su ci moriyar tsarin.
Ya ce tallafin zai basu damar kama sana’oi daban daban domin su zamo masu dogaro da kai.
Dangyatin, ya kuma bayyana cewar mutane kusan ne za su amfana da tallafin kudaden domin bunkasa tattalin arzikinsu.
Kakakin majalisar, ya kuma godewa Gwamna Umar Namadi bisa kyawawan kudurorinsa, gami da kulawarsa wajen ciyar da al’ummar jihar gaba.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Matawalle Ya Bada Tallafin Kudi Da Kayayyakin Abinci Ga Iyalan Marigayi Sarkin Gusau
Ministan Harkokin Tsaron Ƙasa, Dakta Bello Mohammed Matawalle, ya baiwa iyalan marigayi Sarkin Gusau, Alhaji Ibrahim Bello, gudummawar naira miliyan biyar da kuma kayan abinci, bayan rasuwarsa a ranar Alhamis da ta gabata a birnin Abuja sakamakon gajeruwar rashin lafiya.
Dakta Matawalle, ya bayyana alhininsa bisa wannan rashi na Mai Martaba.
Baya ga gudummawar kuɗi, ministan ya kuma bada buhunan shinkafa 20, gero 10, masara 10 da kuma dawa 10 ga iyalan mamacin.
Wata tawaga mai ƙarƙashin jagorancin Sanata Hassan Muhammad Nasiha, tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara a zamanin mulkin Matawalle ne suka miƙa gudummawar a madadin ministan.
Dakta Matawalle ya bayyana marigayi Sarkin Gusau a matsayin shugaba mai ɗabi’a ta gari, wanda ya kasance mai sauƙin kai da tausayi a duk tsawon mulkinsa.
Ya ambato irin jajircewarsa wajen kula da marayu da taimaka musu wajen samun ilimi, inda da dama daga cikinsu suka zama mutane masu amfani a cikin al’umma.
“Rasuwar Sarkin ta bar gibidmai wuyar cika,” in ji Matawalle, yana mai addu’ar Allah Ya jikansa da rahama, tare da baiwa iyalan haƙurin jure rashin.
Da yake karɓar tawagar da gudummawar a madadin iyalan, Hakimin Sunami, Alhaji Mainasara Bello Ciroman Gusau, ya nuna godiya ga ministan bisa wannan gudummawar.
Ya ce masarautar za ta ci gaba da tunawa tare da girmama goyon bayan da Matawalle ke baiwa masarautu, musamman a lokacin da yake gwamna.
Tawagar ta haɗa da fitattun mutane irinsu Ibrahim Umar Dangaladima, Sakataren APC na Jiha; Bashir Idris Ataka, Sakataren Walwala na APC; Mallam Yusuf Idris Gusau, Sakataren Yaɗa Labarai na APC; Ibrahim Maigandi Danmalikin Gidan Goga, Mai ba Minista shawara kan harkokin siyasa, da sauransu.
Haka kuma, Sheikh Tukur Sani Jangebe ya yi addu’ar Allah ya ji ƙan marigayi Sarkin Gusau.
Daga Aminu Dalhatu