Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna ta biya fiye da Mahajjata dubu uku da suka kammala aikin Hajjin shekarar 2023 kudaden da Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON) ta mayar masu.

 

Mai Magana da Manema Labarai na hukumar, Yunusa Mohammed Abdullahi, shine ya bayyana hakan sannan ya kara da cewa an turawa kowane mahajjati ya karɓi sama da naira dubu sittin da ɗaya a asusunsa bakinsa.

 

Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta bayyana cewa an mayar da kudaden ne saboda katsewar wutar lantarki a lokacin da maniyyata ke Muna, wanda ya shafi tsarin sanyaya iska kuma hakan ya janyo musu matsala.

 

Hukumar Alhazai na Jihar Kaduna ta ta yaba da hakurin wadanda har yanzun basu same kudadensu ba, inda ya bayyana cewa jinkirin ya faru ne sakamakon wasu maniyyata ba su bayar da cikakken bayanan asusun ajiyarsu na banki ba.

 

Mallam Yunusa Abdullahi ya tabbatar da cewa an shirya sake fitar da wani zagaye na biyan kudaden a mako mai zuwa, kuma hukumar tana aiki tukuru don tabbatar da cewa dukkan alhazan 2023 da suka cancanta sun karɓi kuɗinsu.

 

Jami’in Hulɗa da Jama’a ya jaddada muhimmancin gabatar da bayanan asusun banki cikin lokaci, yana kira ga duk maniyyatan 2023 da har yanzu ba su karɓi kuɗinsu ba su tuntubi jami’in rijista na ofishin ƙaramar hukumarsu.

 

“Waɗannan bayanai suna da matuƙar muhimmanci don hanzarta mayar da kuɗi ga sauran Mahajjatan,” yana mai jaddada cewa KSPWA na da ƙudirin tabbatar da an biya dukkan kudaden Mahajjatan mudin sun banyarda bayanan asusun bankinsu akan lokaci.

 

Idan baza a manta ba, Shugaban Hukumar, Malam Salihu Abubakar, ya ce, “Mun fahimci muhimmancin mayarda waɗannan kudaden, kuma mun dukufa wajen tabbatar da cewa an kammala rabonsu cikin sauri da gaskiya.”

 

Sanarwar ta bayyana cewa, baya ga kammala biyan kudaden mayarwa na shekarar 2023, hukumar ta riga ta fara mai da hankali kan shirye-shiryen aikin Hajjin bana.

 

Rel/Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Biya Gwamnatin Jihar

এছাড়াও পড়ুন:

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.

 

“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan  
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar