Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna ta biya fiye da Mahajjata dubu uku da suka kammala aikin Hajjin shekarar 2023 kudaden da Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON) ta mayar masu.

 

Mai Magana da Manema Labarai na hukumar, Yunusa Mohammed Abdullahi, shine ya bayyana hakan sannan ya kara da cewa an turawa kowane mahajjati ya karɓi sama da naira dubu sittin da ɗaya a asusunsa bakinsa.

 

Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta bayyana cewa an mayar da kudaden ne saboda katsewar wutar lantarki a lokacin da maniyyata ke Muna, wanda ya shafi tsarin sanyaya iska kuma hakan ya janyo musu matsala.

 

Hukumar Alhazai na Jihar Kaduna ta ta yaba da hakurin wadanda har yanzun basu same kudadensu ba, inda ya bayyana cewa jinkirin ya faru ne sakamakon wasu maniyyata ba su bayar da cikakken bayanan asusun ajiyarsu na banki ba.

 

Mallam Yunusa Abdullahi ya tabbatar da cewa an shirya sake fitar da wani zagaye na biyan kudaden a mako mai zuwa, kuma hukumar tana aiki tukuru don tabbatar da cewa dukkan alhazan 2023 da suka cancanta sun karɓi kuɗinsu.

 

Jami’in Hulɗa da Jama’a ya jaddada muhimmancin gabatar da bayanan asusun banki cikin lokaci, yana kira ga duk maniyyatan 2023 da har yanzu ba su karɓi kuɗinsu ba su tuntubi jami’in rijista na ofishin ƙaramar hukumarsu.

 

“Waɗannan bayanai suna da matuƙar muhimmanci don hanzarta mayar da kuɗi ga sauran Mahajjatan,” yana mai jaddada cewa KSPWA na da ƙudirin tabbatar da an biya dukkan kudaden Mahajjatan mudin sun banyarda bayanan asusun bankinsu akan lokaci.

 

Idan baza a manta ba, Shugaban Hukumar, Malam Salihu Abubakar, ya ce, “Mun fahimci muhimmancin mayarda waɗannan kudaden, kuma mun dukufa wajen tabbatar da cewa an kammala rabonsu cikin sauri da gaskiya.”

 

Sanarwar ta bayyana cewa, baya ga kammala biyan kudaden mayarwa na shekarar 2023, hukumar ta riga ta fara mai da hankali kan shirye-shiryen aikin Hajjin bana.

 

Rel/Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Biya Gwamnatin Jihar

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas

A cewarsa, gobarar na iya kasancewa ta samo asali ne daga wani gini da ke bayan gidan man.

Rahotanni sun nuna cewa gobarar na iya tashi ne daga tankunan mai da ke ƙasa, kafin ta bazu zuwa cikin gidan man gaba ɗaya.

Hukumar kashe gobara ta jihar ta yi gaggawar killace wajen domin hana cunkoso da tabbatar da tsaron jama’a yayin aikin kashe gobarar.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobarar, Shakiru Amodu, ya tabbatar da cewa an samu nasarar kashe gobarar kafin ta bazu zuwa gidajen da ke kusa.

Kafin ƙarfe 6 na yamma, jami’an agajin gaggawa sun shawo kan lamarin gaba ɗaya, tare da killace yankin da abin ya shafa domin kaucewa wata barazana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
  • Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita
  • Gini ya kashe Ba’indiye a Zariya
  • Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai