Leadership News Hausa:
2025-06-26@22:46:48 GMT

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (5)

Published: 1st, February 2025 GMT

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (5)

Hakanan ma akwai su yi aiki duk irin halin da suka samu kansu, su san yadda lamurran ilimi za su tafi kamar yadda ya dace.Ko mai dai menene hanyoyin ko wuraren da jami’an ilimi za su iya yin aiki suna da yawa da kuma yadda za su samu ci gaba ta kowane hali suka tsinci kansu.Ko dai suna aiki a makarantar lardi ko hukumar da ke karkashin gwamnati,ko hukumar wadda ita babu ruwanta da riba, jami’an ilimi suna taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da duk wadanda suke son ilimi ana koya masu ta nagartattar hanyar da za ta kasance da hanyoyin karuwa.

 

Irin ayyukan da jami’in ilimi zai iya yi

Jami’inilimi kwararre ne wanda kuma har ila yau alhakin tafiyar harkokin,manufofin,da tsare- tsaren ilimi suka rataya a wuyansa, wannan ma har ya hada da yadda za a cimma nasarar yin hakan.Suna yin ayyuka a hukumomi daban- daban da suka hada da makarantu, kwalejoji, jami’oi, da kuma hukumomin gwamnati.Babban aikin su shi ne samar da kuma gabatar da tsare- tsare wadanda za su taimakawa ci gaban lamurran ilimi.Hakanan ma suna aiki kafada- kafada da Malamai, ‘yan makaranta, Iyaye, da sauran masu fada aji, domin tabbatar da cewar na tafiyar da lamurran ilimi kamar yadda ya dace, su kuma wadanda ake koyawa suna fahimtar abinda ake koya masu. Hakanan ma ayyukan da za su iya yi jami’an ilimi suna da yawa sun kuma sha bamban.Suna ma iya yin aiki a bangarorin kamar su yadda za a tsara ci gaban koyarwa, horar da Malami,yadda za a rika bibiyar tsarin ilimi, da kuma binciken ilimi.Jami’an ilimi suna iya kasancewa wadanda suka kware a fannoni ko bangarori daban daban kamar karatun/ilimin rayuwar farko ta yaro, bangaren yaki da jahilci, ilimi na musamman, da kuma ilimin koyon sana’oi.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC ya kama manyan jami’an NNPC kan badaƙalar Dala 7.2bn

Hukumar EFCC mai yaki da masu karya tattalin arziki ta tsare wasu tsofafin manyan jami’an Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) kan zargin badakalar kudade da yawansu ya kai Dala biliyan 7.2.

Jami’an EFCC sun tsare tsohon Babban Jami’in Kudi na NNPCL, Umar Ajiya Isah da kuma tsohon Manajan-Daraktan Matatar Mai ta Warri, Jimoh Olasunkanmi, kan zargin almundahanar.

Wani babban jami’in EFCC da ya nemi a boye sunansa ya ce hukumar ta tsare tsoffin manyan jami’an na NNPC ne kan zargin wadaka da kudaden gyaran matatun mai da ke Kaduna da Warri da kuma Fatakwal.

Wakilinmu ya yi kokarin samun karin haske daga kakakin EFCC, Dele Oyewale, amma jami’in bai amsa duk kiraye-kirayen da aka yi masa da kuma rubutattun sakon da aka tura masa domin samun bayani a hukumance.

Umar Ajiya ya kasance mai kula da harkokin kula da kudaden gyaran matatun guda uku da kuma da kuma manyan jami’an da ke aiki.

Iran ta kama ’yan leƙen asirin Isra’ila 6 Iyalan Kanawa da aka kashe a Uromi sun zargin gwamnati da yin watsi da su

Wani jami’in EFCC ya bayyana cewa hukumar tana kuma bincikar was jami’an NNPC da ke kula da wasu muhimman ayyuka kan zargin su da karkatar da kudade da kuma karbar na-goro daga ’yan kwangila.

A cewarsa, wadanda binciken ya shafa sun hada da Manajan-Daraktan Matatar Warri, Tunde Bakare; tsohon Manajan-Daraktan Matatar Fatakwal, Ahmed Adamu Diko da wani tsohon Manajan-Daraktan matatar, Ibrahim Monday Onoja.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙarancin Abinci: UNICEF ta tallafa wa yara 600,000 a Borno da Yobe
  • Ƙarancin abinci: UNICEF ta tallafawa yara 600,000 a Borno, Yobe
  • Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
  • An tallafawa iyalan jami’an ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
  • Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno
  • EFCC ya kama manyan jami’an NNPC kan badaƙalar Dala 7.2bn