Leadership News Hausa:
2025-05-02@04:49:53 GMT

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (5)

Published: 1st, February 2025 GMT

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (5)

Hakanan ma akwai su yi aiki duk irin halin da suka samu kansu, su san yadda lamurran ilimi za su tafi kamar yadda ya dace.Ko mai dai menene hanyoyin ko wuraren da jami’an ilimi za su iya yin aiki suna da yawa da kuma yadda za su samu ci gaba ta kowane hali suka tsinci kansu.Ko dai suna aiki a makarantar lardi ko hukumar da ke karkashin gwamnati,ko hukumar wadda ita babu ruwanta da riba, jami’an ilimi suna taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da duk wadanda suke son ilimi ana koya masu ta nagartattar hanyar da za ta kasance da hanyoyin karuwa.

 

Irin ayyukan da jami’in ilimi zai iya yi

Jami’inilimi kwararre ne wanda kuma har ila yau alhakin tafiyar harkokin,manufofin,da tsare- tsaren ilimi suka rataya a wuyansa, wannan ma har ya hada da yadda za a cimma nasarar yin hakan.Suna yin ayyuka a hukumomi daban- daban da suka hada da makarantu, kwalejoji, jami’oi, da kuma hukumomin gwamnati.Babban aikin su shi ne samar da kuma gabatar da tsare- tsare wadanda za su taimakawa ci gaban lamurran ilimi.Hakanan ma suna aiki kafada- kafada da Malamai, ‘yan makaranta, Iyaye, da sauran masu fada aji, domin tabbatar da cewar na tafiyar da lamurran ilimi kamar yadda ya dace, su kuma wadanda ake koyawa suna fahimtar abinda ake koya masu. Hakanan ma ayyukan da za su iya yi jami’an ilimi suna da yawa sun kuma sha bamban.Suna ma iya yin aiki a bangarorin kamar su yadda za a tsara ci gaban koyarwa, horar da Malami,yadda za a rika bibiyar tsarin ilimi, da kuma binciken ilimi.Jami’an ilimi suna iya kasancewa wadanda suka kware a fannoni ko bangarori daban daban kamar karatun/ilimin rayuwar farko ta yaro, bangaren yaki da jahilci, ilimi na musamman, da kuma ilimin koyon sana’oi.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”

 

To, bayanai a sama sun nuna ra’ayi iri daya na gwamnatocin dimbin kasashe masu tasowa. Ban da haka, wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar yada labarai ta Sin CGTN, da jami’ar Renmin ta kasar Sin suka gudanar a kasashe 38, ya nuna cewa, matakan ramuwar gayya da kasar Sin ta dauka kan kasar Amurka suna samun goyon baya tsakanin al’ummun kasashe daban daban, inda a dimbin kasashe masu tasowa da suka hada da Najeriya, da Kenya, da Masar, da Ghana, da Afirka ta Kudu, da Turkiya, matakan kasar Sin suka samu goyon baya daga mutane fiye da kaso 70% da aka gudanar da bincike kansu. Kana a kasashen yamma da suka hada da Faransa, da Jamus, da Canada, da Birtaniya, da dai sauransu, jimillar ta kai tsakanin kaso 65.5% zuwa 70.5%.

 

Sai dai kasar Sin ba ta son yakin ciniki, ko da yake tana wakiltar ra’ayi mai adalci na akasarin kasashe. Kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce, “Babu mai samun nasara a yakin harajin fito, da na ciniki.” Amma, bisa la’akari da cewa kasar Amurka ce ta ta da yakin ciniki, to, kasar Sin ba za ta taba mika wuyarta ba, kuma ba za ta yi hakuri da matakin cin zarafi ba. Sin ta nanata cewa, idan kasar Amurka na son daidaita al’amarin ta hanyar tattaunawa, to, ya kamata ta “daina barazana da matsin lamba, ta yi tattaunawa bisa tushen daidaito, da mutunta juna, da amfanawa juna.”

 

Hakika, ban da wadannan abubuwan da aka ambata, don kaddamar da tattaunawa, ana bukatar sanin ya kamata, wanda kasar Amurka ta rasa. Misali, yadda kasar Amurka ta janye jikinta daga dimbin kungiyoyin kasa da kasa, da yarjeniyoyin duniya, da daina samar da tallafi ga sauran kasashe, sun nuna yunkurinta na kaucewa daukar nauyi sakamakon raguwar karfinta a fannin tattalin arziki. Sai dai wannan yanayi mai kunci bai hana ta ci gaba da neman ba da umarni ga sauran kasashe, da cin zarafinsu ba. Ban da haka, mu kan ga yadda shugabannin kasar Amurka suke ba da umarni da gyara shi cikin sauri, da yin karairayi yadda suka ga dama, da wulakanta takwarorinsu na sauran kasashe, da kasa kare bayanan sirrin da suka shafi yaki, wadanda suka nuna gazawarsu wajen aiki. Ma iya cewa, yanzu haka, kasar Amurka tamkar damisar takarda ce, mai ban tsoro amma maras karfi.

 

Za mu jira lokacin da za a iya komawa teburin shawarwari don tattauna batun kawo karshen yakin ciniki, inda za a jira har zuwa lokacin da kasar Amurka za ta gamu da dimbin matsaloli, ta yadda za ta yi watsi da matakan zalunci, da sake samun sanin ya kamata. Amma yanzu muna iya tabbatar da matakin da ya kamata kasashe masu tasowa su dauka, wato karfafa hadin kansu, maimakon mika wuya ga kasar Amurka, wadda ta kasance tamkar wata “damisar takarda”, da ke neman cin zarafin sauran kasashe, da ta da rikici a duniya. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Kashi Na Uku Na Canton Fair Karo Na 137 
  • Sojoji sun ceto fasinjoji 99 daga hatsarin kwale-kwale a Ribas
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta
  • Dubban Mutanen Burkina Faso Sun Yi  Gangamin Nuna Goyon Bayan Shugaban Kasa Ibrahim Traore
  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana