Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (5)
Published: 1st, February 2025 GMT
Hakanan ma akwai su yi aiki duk irin halin da suka samu kansu, su san yadda lamurran ilimi za su tafi kamar yadda ya dace.Ko mai dai menene hanyoyin ko wuraren da jami’an ilimi za su iya yin aiki suna da yawa da kuma yadda za su samu ci gaba ta kowane hali suka tsinci kansu.Ko dai suna aiki a makarantar lardi ko hukumar da ke karkashin gwamnati,ko hukumar wadda ita babu ruwanta da riba, jami’an ilimi suna taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da duk wadanda suke son ilimi ana koya masu ta nagartattar hanyar da za ta kasance da hanyoyin karuwa.
Irin ayyukan da jami’in ilimi zai iya yi
Jami’inilimi kwararre ne wanda kuma har ila yau alhakin tafiyar harkokin,manufofin,da tsare- tsaren ilimi suka rataya a wuyansa, wannan ma har ya hada da yadda za a cimma nasarar yin hakan.Suna yin ayyuka a hukumomi daban- daban da suka hada da makarantu, kwalejoji, jami’oi, da kuma hukumomin gwamnati.Babban aikin su shi ne samar da kuma gabatar da tsare- tsare wadanda za su taimakawa ci gaban lamurran ilimi.Hakanan ma suna aiki kafada- kafada da Malamai, ‘yan makaranta, Iyaye, da sauran masu fada aji, domin tabbatar da cewar na tafiyar da lamurran ilimi kamar yadda ya dace, su kuma wadanda ake koyawa suna fahimtar abinda ake koya masu. Hakanan ma ayyukan da za su iya yi jami’an ilimi suna da yawa sun kuma sha bamban.Suna ma iya yin aiki a bangarorin kamar su yadda za a tsara ci gaban koyarwa, horar da Malami,yadda za a rika bibiyar tsarin ilimi, da kuma binciken ilimi.Jami’an ilimi suna iya kasancewa wadanda suka kware a fannoni ko bangarori daban daban kamar karatun/ilimin rayuwar farko ta yaro, bangaren yaki da jahilci, ilimi na musamman, da kuma ilimin koyon sana’oi.
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda ɗan shekara 70 ya rasu a gobarar tankokin gas a Zariya
Wani dattijo ya rasu a sakamakon hatsari da gobarar tankokin sakon iskar gas da ta auku a yankin Zariya da ke Jihar Kaduna.
Aliyu Ramalan Babbale mai shekara sama da 70 ya rasu ne a lokacin da yake ƙokarin tsira da ransa a sakamakon hatsarin tankokin a safiyar ranar Litinin.
Dattijon ya gamu da ajalinsa ne a kan hanyarsa na zuwa gona, lokacin da wasu tankokin dakon gas biyu suka kama da wuta bayan su gogi juna.
Mai auran babban ’yar marigayi Malam Abdullahi Magaji, ya yi wa Aminiya bayanin yadda lamarin ya faru, akan rasuwar marigayin.
ya ce, “A jiya da safe marigayin yana kan babur ne a kan hanyarsa na zuwa gona, sai waɗannan motocin ɗakon man gas ɗin suka kama da wuta kuma suka yi ƙara.
“To a lokacin da yake ƙokarin tsira da rai ne wani shi ma da yake kan babur garin gudu sai ya kwashe shi a inda kafin a kai shi asibitin ya rasu,” in ji shi.
Marigayi ya rasu ya bar mata biyu da ’ya’ya shida kuma tuni aka yi jana’izarsa a gidansa da ke Babbale cikin birnin Zariya.
Bayanai na ƙara fitowa dangane da wadanda suka rasu a sanadiyar hatsarin tankokin dakon gas ɗin da ya auku a garin Zariya.