Aminiya:
2025-05-01@04:47:30 GMT

APC ta kori tsohon Gwamnan Osun, Aregbesola daga jam’iyyar

Published: 1st, February 2025 GMT

Jam’iyyar APC a Jihar Osun, ta kori Tsohon Gwamnan Jihar kuma Tsohon Ministan Cikin Gida, Rauf Aregbesola, bisa zargin cin amanar jam’iyyar.

Wannan ya biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da shugabannin jam’iyyar na Ƙaramar Hukumar Ilesa ta Gabas suka gabatar.

Yadda Kano ta koma matattarar ’yan TikTok bayan Hisbah ta daina kamensu Muna da ƙarfin aljihun ɗaukar nauyin Taron Al-Ƙur’ani —Sheikh Bala lau

Sun nemi a ɗauki mataki a kan Aregbesola saboda zargin kafa ƙungiyoyin da ke raba kan jam’iyyar da yin haɗin gwiwa da jam’iyyun adawa don raunana APC a Osun.

A cikin wata wasiƙa da kwamitin zartarwa na APC na Osun ya aike wa shugaban jam’iyyar na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, sun bayyana cewa Aregbesola ya kafa wata ƙungiya mai suna “Omoluabi Caucus” ba tare da amincewar jam’iyyar ba.

Sannan ya yi furuci na ɓatanci ga shugabannin jam’iyyar, ciki har da Shugaba Bola Tinubu, tsohon gwamna Bisi Akande, da kuma tsohon gwamna Gboyega Oyetola.

Kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar ya rubuta wa Aregbesola wasiƙa, inda suka ba shi sa’o’i 48 ya mayar da martani kan zarge-zargen da ake masa.

Sai dai Aregbesola bai yi wani jawabi ba kan hakan ba, wanda ya sa jam’iyyar ta ɗauki matakin korarsa.

Wannan rikici ya ƙara nuna yadda rikicin cikin gida ke ƙara tsamari a jam’iyyar APC a Jihar Osun, musamman dangane da bambance-bambancen da ke tsakanin Aregbesola da wasu shugabannin jam’iyyar a matakin jiha da na ƙasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aregbesola Jihar Osun Kora Siyasa tsohon gwamna a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe

Shugaban tawagar baƙin, Alhaji Ibrahim Abdullahi Yar’adua, ya ce sun zo Yobe domin nazarin halin tsaro da tattara bayanai da za su taimaka wajen tsara manufofin tsaron ƙasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai