Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Bayyana Matakan Da Amurka Zata Bi Don Kyautata Dangantaka Da Iran
Published: 1st, February 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Aragchi yana bayyana matakan da sabuwar gwamnatin Amurka zata dauka idan har tana son sake samun yardar samun yardar kasar Iran.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a lokacinda yake hira ta musamman da tashar talabijin ta Al-jazeera ta kasar Qatar a birnin Doga.
Ministan ya kara da cewa gwamnatocin Amurka da suka shude daga ciki har da gwamnatin Trumps suka yi a baya musamman ficewarta su daga yarjeniyar JCPOA.
Abbas Argchi ya bayyana cewa abu mafi muhimmanci wanda dole ne Amurka ta yi idan tana son jawo hankalin iran dangane da tattaunawa da ita shi ne sako kudaden ta masu yawa wadanda ta hana a yi amfani da su a wurare da dama a duniya.
Ministan ya ce wannan yana iya zama mataki na faro wanda gwamnatin Amurka zata iya dauka idan tana son haka.
Kafin haka dai gwamnatin sabuwar gwamnatin Amurka tana ganin tattaunawa da kasar Iran ita, tana ganin hanyar da zata da ita, don warware matsaloli daban-daban da suke tsakaninsu. A wannan karon.
Sannan ya kara da cewa idan har tana son al-amura su tafi mata yadda take so, ya kasance tattaunawar ta shirin nukliyar kasar Iran ta zaman lafiya ce kadai za’a yi magana a kansa, kada ta hana da wasu al-amura, musamman rawar da irin take takawa a yankin Asiya ta kudu.
Kafin haka dai gwamnatin Donal Trumps a zagayen na farko ne ta fidda Amurka daga yarjeniyar JCPOA wacce aka kulla da gwamnatin Obama a shekara ta 2015, kuma ta fice daga cikinta a shekara ta 2018 sannan ta sake dorawa kasar takunkuman tattalin arziki mafi muni a tarihin kar wadanda suke aiki har yanzun.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
Yau Litinin, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Guo Jiakun, ya shirya taron manema labaru na yau da kullum.
A wajen taron, wani dan jarida ya yi tambaya game da sabuwar yarjejeniyar kasuwanci da aka kulla tsakanin Amurka da kungiyar EU. A yayin da yake ba da amsa, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin a ko da yaushe tana ba da shawarar cewa, ya kamata dukkan bangarori su warware bambance-bambancen tattalin arziki da cinikayya ta hanyar tattaunawa, domin kiyaye yanayin hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa.
Bugu da kari, dangane da taron tattauna batun tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka a kasar Sweden, Guo Jiakun ya bayyana cewa, matsayin kasar Sin kan batutuwan da suka shafi tattalin arziki da cinikayya a bayyane yake. Ana sa ran Amurka za ta yi aiki tare da kasar Sin wajen aiwatar da muhimman shawarwarin da shugabannin kasashen biyu suka cimma a wata tattaunawa ta wayar tarho.
Game da rikicin kan iyakar kasashen Cambodia da Thailand, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin za ta tsaya tsayin daka wajen tabbatar da gaskiya da adalci, da ci gaba da yin cudanya da kasashen Cambodia da Thailand, da sa kaimi ga zaman lafiya da tattaunawa.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp