Fizishkiyan: Gwagwarmaya Za Ta Yi Karfin Da Ba Za Iya Rusa Ta Da Makamai Ba
Published: 1st, February 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana cewa; babbar matsalar da duniyar musulmi ke fuskanta ta samo tushe ne daga yin isa daga koyarwar musuluncin, da babu abinda hakan ya haddasa sai rabuwar kawuna da sabani, ya kuma bai wa makiya kafar da za su shiga.
Shugaban kasar ta Iran wanda ya aike da sako zuwa wurin rufe ‘gasar karatun akur’ani mai girma karo na 41 da aka yi a birnin Mashhad, ya bayyana cewa; Alkur’ani mai girma yana yin Magana ne da musulmi a matsayin al’umma daya dunkulalliya, yake kuma yin kira a gare su da su yi riko da igiyar Allah da hadinkai, domin hana rabuwar kawuna.
Shugaban na kasar Iran ya kuma ce; Shakka babu, wani sashe mai girma na matsalolin da duniyar musulmi take fuskanta a wannan lokacin sakamako ne na nesantar koyarwar al’kur’ani, wanda kuma babu abinda hakan yake haifarwa sai rabuwar kawuna da kuma bude kafa a gaban makiya ‘yan adamtaka.”
Shugaba Fizishkiyan ya kuma ce; shi alkur’ani mai girma yana yin Magana ne da dukkanin bil’adama ba tare da la’akari da launinsu ko ajinsu ba, ko kuma addinin da suke yi,kuma ya nuna wa jinsin dan’adam hanyar kai wa ga kamala.
Haka nan kuma shugaban na kasar Iran ya ce, a karkashin koyarwar addinin musulunci, mutane za su sami madogara mai karfi mai nagarta a cikin wannan duniyar da take cike da rudani.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
Dan majalisa mai suna muhammad Mirzai ya ce; Kasashen turai sun zaku, akan su sami bayanai akan girman asarar da aka yi wa cibiyoyin Nukiliyar Iran don haka ya zama wajibi Iran din ta yi amfani da siyasar barinsu a cikin duhu.
A yayin zaman da majalisar shawarar musulunci ta Iran ta yi a yau Talata, dan majalisar ya kuma yi bayani akan kallafaffen yakin kwanaki 12, ya yi ishara akan yadda HKI ta yi amfani da kirkirarriyar fasaha da kuma wasu hanyoyi na leken asiri,amma duk da haka ta ci kasa, saboda jagoranci mai cike da fasaha na jagora, da kuma yadda al’ummar kasar ta yi tsayin daka da goyon bayan tsarin musulunci.
Haka nan kuma ya ce; Daga cikin manufofin da HKI ta Shata cewa za ta cimmawa a yayin yakin, shi ne samar da sauyi a cikin wannan yankin, shi ya sa da dama daga cikin hukumomin kasashen larabawa su ka fahimci cewa raunana Iran yana nufin raunana kasashensu.