Ɗan Ibo ya yi lalata da ’yan firamare biyu a Zariya
Published: 31st, January 2025 GMT
Ana zargin wani ɗan ƙabilar Ibo mai suna Oguchwku da yin lalata yaran makarantar Firamare masu shekaru 9 da 10 da haihuwa, kuma ‘ya’yan Hausawa ne.
Aminiya ta bibiyi lamarin a inda ta garzaya Cibiyar Kula da cin zarafin mata da ƙananan yara da ke Asibitin Gambo Sawaba Ƙofar Gayan Zariya a Jihar Kaduna.
Daraktan cibiyar Salama Centre da ke Asibitin Gambo Sawaba ƙofar Gayan Zariya, Hajiya Aishatu Ahmad, ta shaida wa Wakilin namu cewar a ranar 27 ga watan ɗaya na wannan shekarar ne hukumar ‘yan sanda da ke Kasuwar Mata a ƙaramar hukumar Sabon Gari ta kawo wani mai suna Oguchwku Cibiyarsu tare da wasu yaran Makarantar Firamare ta Jafaru LEA su biyu.
Daraktar ta ce, bayan kammala binciken yaran, bincike ya nuna cewa an yi lalata da su.
Daraktan cibiyar Hajiya Aishatu Ahmad ta ce, sun ɗora yaran akan magani, kuma sun ba ‘yan sanda sakamakon, tare da tura ƙwafin sakamakon zuwa ga Kwamishinan jinƙai da walwala ta jihar Kaduna domin ɗaukar mataki.
Babban jami’I a ofishin ‘yan sanda na Kasuwar Mata ya ce duk da taƙardama akan rashin yarda da sakamakon binciken da Asibitin Gambo Sawaba da iyalan wadda ake zargin suka yi sai na sake tura su asibitinmu na musamman domin ƙara binciken kuma yanzu haka mun tura su zuwa Kaduna.
Duk ƙoƙarin kiran wayar, mai magana da yawan rundunar ‘yan sanda jihar Kaduna ASP Mansur Hassan, tare da tora saƙon karta kwana amma har zuwa wannan lokacin bai amsa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar Christopher Musa
Majalisar Shugabannin Kudancin Kaduna (SKLC) ta kammala shirye-shirye domin gudanar da gagarumar tarbar ga tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa (mai ritaya).
Za a yi bikin ne domin tunawa da kyakkyawar rawar da majalisar ta ce ya taka a aikin soja da kuma hidimarsa ga kasa.
An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aureAn shirya gudanar da bikin ne a ranar Asabar, 22 ga watan Nuwamba, 2025, a Babban Filin Wasan na garin Kafanchan, cibiyar kasuwancin Kudancin Kaduna.
A yayin taron majalisar karo na 19 da aka gudanar a Kafanchan, Shugaban SKLC, Ishaya Dare Akau, ya ce za a ba Janar Musa lambar yabo mafi girma ta majalisar wato GCSK.
Akau, ya ce wannan karramawar tana nuni da yadda Janar Musa ya wakilci Kudancin Kaduna, Jihar Kaduna, da Najeriya baki daya cikin kwarewa da cancanta, inda ya bayyana shi a matsayin jakada nagari.
A yayin taron, majalisar ta kuma kaddamar da kwamitin kula da harkokin kudi na Bikin Gargajiya na Shekara-shekara na Kudancin Kaduna (SKFEST), inda aka nada Shugaban Hukumar Haraji ta Jihar Kaduna (KADIRS), Comrade Jerry Adams, a matsayin shugaban kwamitin.
Manyan jami’an gwamnati da dama sun halarci taron karkashin jagorancin Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Henry Danjuma Magaji, tare da Mai ba Gwamna shawara kan harkokin siyasa, Hon. Ado Dogo Audu.
Sun yi wa majalisar bayani kan muhimman shirye-shiryen gwamnati, ciki har da amincewar da gwamnatin tarayya ta bayar na farfado da aikin gina hanyar Jere–Kagarko–Jaba–Kwoi–Kafanchan, wadda Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya taimaka wajen ganin tabbatuwarsa.