Aminiya:
2025-09-17@23:28:06 GMT

Tubabbun ’yan Boko Haram 5,000 sun koma cikin jama’a

Published: 31st, January 2025 GMT

Mayaƙan Boko Haram aƙalla 5,000 da suka tuba sun koma cikin al’umma da iyalansu, a cewar Cibiyar Yaƙi da Ta’addabnci na Ƙasa.

Cibiyar, wadda ke ƙarƙashin Ofishin Mashawarcin Shugaban Ƙasa Kan Sha’ani Tsaro ta bayyana cewa babu ko mutum ɗaya da cikin tubabbun mayaƙan na Boko Haram da ya sake ɗaukar makami.

Ta bayyana cewa gwamnatin Jihar Borno ta tabbatar cewa wata shida bayan kammala ba su horo da sauya tunanin tsofaffin mayaƙan, amma har yanzu babu labarin ko mutum ɗaya daga cikinsu da ya yi tubar muzuru.

Shugabar Sashen Daƙile Rikice-rikice Masu Alaƙa da Tsattsauran Ra’ayi (PVEA)  ta Cibiyar, Ambasada Mairo Musa Abbas, ce ta bayyana haka a yayin taron gwamnonin yankin Tafkin Chadi a Maiduguri, Jihar Borno.

NAJERIYA A YAU: Anya Jam’iyyar PDP Za Ta Kai Labari A Fagen Siyasar Najeriya Kuwa? KAROTA za ta kashe N250m wajen gyaran motoci 5 a Kano Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-Rufai

Da take jawabi kan kula da masu ficewa daga Boko Haram da kuma  kawo ƙarshen kungiyoyi masu ɗaukar makamai, Ambasada Mairo ta jaddada muhimmancin amfanin da matakai da dabaru na bai-ɗaya a tsakanin gwamnonin ya kin domin magance matsalar tsaron.

Ta ce shirin Operation Safe Corridor da ke karɓa ta tare da sauya tunanin tubabbun ’yan Boko Haram ya yi nasarar sauya tunanin tsofaffin mayaƙan ƙungiyar guda 5,000.

A cewarta, Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) tana aiki da sarakunan gargajiya da malaman addini a duk ƙananan hukumomi 774 da ke faɗin ƙasar nan domin sanya ido kan yanayin rayuwar tubabbun mayaƙan da suka dawo cikin al’umma.

Ta kuma jinjina wa tsarin da Gwamnatin Jihar Borno ta jagoranta kan tubabbun mayaƙan da masu tsattsauran ra’ayi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Mayaƙan Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

 

Ya ce, masu garkuwa da mutanen sun afka gidansa ne a daren Lahadi a lokacin da mazauna gidan ke shirin kwanciya barci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin