DR Congo: Sojoji sun ƙaddamar da gagarumin hari kan ’yan tawayen M23 —Shugaba Tshisekedi
Published: 30th, January 2025 GMT
Shugaba Felix Tshisekedi na Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo, ya bayyana cewa sojojin ƙasar na tunkarar ’yan tawayen M23 da suka kaɗɗammar da munanan hare-hare tare da ƙwace ikon muhimman wurare a Birnin Goma da ke gabashin ƙasar.
Hare-haren mayaƙan M23 da ke samun goyon bayan ƙasar Rwanda sun kashe Gwamnan Birnin Goma, a makon jiya a yayin da dubban mutane ke gudun hijira domin tsira da rayukansu.
A ranar Laraba mayaƙan M23 suka ƙwace wasu yankuna biyu a Lardin Kivu da ke gabashin ƙasar, daga hannun sojoji.
A jawabinsa na ranar Laraba ta talabijin, Shugaba Tshisekedi ya zargi ƙasashen duniya kan rashin ɗaukar mataki kan lamarin, musamman hannun Rwanda a cikin lamarin, wanda ya ce katsalandan ne ga dimokuraɗiyya kuma yana iya ƙara munin al’amarin.
NAJERIYA A YAU: Ainihin Dalilan Taƙaddama Kan Kafa Kotunan Musulunci A Kudu Za a dawo da ’yan Najeriya sama da 5,000 da ke zaune a AmurkaƘazancewar halin da ke ciki a Gabashin kasar ta DR Congo ya haifar da fargabar ƙara taɓarɓarewar yanayin rayuwar ’yan gudun da matsalar abubuwan more rayuwa a ƙasar.
Amma a ranar Laraba Shugaba Tshisekedi ya bayyana cewa ’yan tawayen suna ɗanɗana kuɗarsu a hannun sojojin ƙasar mai arziƙin zinare da lu’ulu da sauran ma’adinai.
Shugaba Felix Tshisekedi, a jawabinsa na farko tun bayan faruwar hare-haren na M23 a tsawon makonni, ya bayyana cewa sojojin sun samu gagarumar nasara.
Gabashin ƙasar Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo ya shafe shekaru sama da 30 yana fama rikici inda ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai ke addabar al’umma, baya ga tawaye ga gwamnati.
Ana alaƙanta wanna rikici da kisan kiyashi da aya auku a shekarar 1994 lokacin yaƙin basasa ƙasar Rwanda, maƙwabciyar DR Congo.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Mayaƙan M23 Rwanda
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a yi taro karo na hudu na shawarwari tsakanin Tehran da Washington kan shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Rome na kasar Italiya a ranar Asabar mai zuwa.
M. Araghchi ya fadawa manema labarai a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin kasar na mako-mako yau Laraba cewa, inda ya ce taron na Rome zai kasance gabanin wani taro a ranar Juma’a na tsakanin Tehran da kasashen Turan nan uku da ake wa lakabi da E3 wato – Ingila, Faransa da kuma Jamus wadanda suka sanya hannu kan yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015.
Ya ce rawar da kasashen Turai uku ke takawa ta ragu sakamakon manufofinsu a tattaunawar da aka dade ana yi, don haka a shirye muke mu gudanar da zagaye na gaba na shawarwari da su a birnin Rome.
Babban jami’in diflomasiyyar ya kara da cewa, Tehran na da burin warware batun nukiliyarta cikin lumana.”
Da aka tambaye shi game da halin da ake ciki na baya-bayan nan na kudaden da Iran ta toshe saboda takunkumin da kasashen yamma suka kakaba mata, Araghchi ya ce daskararrun kudaden na daga cikin takunkumin da ya zama dole a dagewa iran.
Kawo yanzu Iran da Amurka sun yi tattaunawa har uku ta farko a Oman, ta biyu a Italiya sai kuma wace aka gudanar a ranar Asabar data gabata a Oman.
Dukkanin bangarorin na cewa akwai fata mai kyau a jerin tattaunawar da suka gabata.