Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Zata Kalubalanci Duk Wanda Ya Kai Hari Kan Cibiyoyin Nukiliyarta
Published: 29th, January 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Duk wani hari da aka kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran zai fuskanci mayar da martani cikin gaggawa
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Harin da Amurka da yahudawan sahayoniyya suke kai wa kan cibiyoyin nukiliyan kasashe, nau’in hauka ne kuma zai jefa yankin cikin bala’i.
A cikin wata sanarwa da ya aikewa gidan talabijin na Sky News a ranar Talata, Araqchi ya sake jaddada matsayin Iran na cewa: “Duk wani hari da za a kai wa cibiyoyin nukiliyar kasarsa zai fuskanci mayar da martani cikin gaggawa da azama,” ya kara da cewa: “Ba ya jin za a aiwatar da irin wannan aikin wauta kan Iran, hasali ma, hakan wani nau’in hauka ne kuma zai wurga yankin cikin mummunan bala’i.”
Dangane da yiwuwar tattaunawa da Amurka da kalaman shugaban Amurka Donald Trump game da warware takaddamar ta hanyar diflomasiyya, Araqchi ya jaddada cewa: “Sabuwar yarjejeniyar da za a kulla da Iran zata kasance mai kyau.” Ya kara da cewa: yanayi ya canja da matakan baya saboda akwai ayyuka masu yawa wanda dole ne ga ɗaya bangaren ya ɗauki matakin dawo da kwarin gwiwa, duk da har yanzu Iran ba ta ji komai daga gare shi ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Gwamnan Jihar Filato, Barr. Caleb Mutfwang, ya bayyana cewa babu wata ƙaramar hukuma a cikin jihar da ƴan ta’adda ko ƴan bindiga ke da iko da ita. Ya bayyana hakan ne a yayin wata ganawa da ƴan jarida da aka gudanar a sabon gidan gwamnati da ke Little Rayfield, Jos, a ranar Talata.
Gwamna Mutfwang ya ce gwamnatinsa ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da matsalar tsaro, musamman ta hanyar farfaɗo da rundunar tsaron cikin gida ta jihar wato Operation Rainbow, domin tallafa wa sauran hukumomin tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Ana Ci Gaba Da Alhinin Mutuwar Malam Adamu Fika Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A FilatoYa ƙara da cewa, gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen ganin an dawo da zaman lafiya a sassan jihar da rikice-rikicen ƙabilanci ko na addini suka taɓa. Ya ce gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro da shugabannin gargajiya domin tabbatar da fahimtar juna da daidaiton al’umma.
Gwamnan ya sake jaddada buƙatar kafa ƴansandan jiha, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen rage matsalolin tsaro a faɗin Nijeriya. Ya ce kafa ƴansandan jiha zai bai wa gwamnatocin jihohi damar yin tsari da ɗaukar matakan da suka dace da yanayin tsaron yankunansu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp