Haka kuma, an naɗa Muhammad Yahaya Liman a matsayin sabon Daraktan Akanta.

Ya samu ƙwarewa a fannonin rahoton kuɗi da sarrafa kuɗi, ana sa ran zai taimaka wajen ƙara ƙarfin tsarin kuɗi na jihar.

An kuma naɗa Akibu Isa Murtala, wanda a baya ya kasance Mataimaki na Musamman a Ofishin Shugaban Ma’aikata, a matsayin Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Gudanarwa.

Aikin sa shi ne kula da gudanar da ayyukan ma’aikatu.

Injiniya Abubakar Sadiq kuma an naɗa a matsayin Mataimakin Manajan Darakta na Hukumar Samar da Ruwa da Tsabtace Muhalli a Ƙauyuka (RUWASA).

An ɗora masa alhakin inganta samar da ruwa da tsabtace muhalli a yankunan karkara.

Haka kuma, an kafa kwamiti na musamman domin farfaɗo da Hukumar Sufuri ta Jihar Kano (Kano Line).

Sa’idu Abdullahi Shu’aibu zai jagoranci kwamitin a matsayin Shugaba kuma Muƙaddashin Manajan Darakta, inda za su duba tare da tsara ayyukan Kano Line cikin watanni shida masu zuwa.

Gwamna Abba ya yi kira ga dukkanin sabbin jami’an da aka naɗa da su jajirce tare da nuna ƙwarewa, amana, da gaskiya wajen gudanar da ayyukansu.

Ya sake jaddada muhimmancin rawar da za su taka wajen ci gaban Jihar Kano.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnatin

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi

Gwamnatin jihar Kano tare da hadin gwiwar wata kungiya mai suna Partnership for Agile Governance and Climate Change (PACE) ta kaddamar da manufofinta na sauyin yanayi a hukumance. Wannan manufa mai mahimmanci ta samar da taswirar dabaru don ragewa, daidaitawa, da tsarin tafiyar da yanayi mai hadewa a duk sassan ci gaba a jihar.

 

Da yake jawabi a wajen taron kaddamar da taron wanda aka gudanar a dakin taro na Armani Event Centre dake Kano, Gwamna Abba Yusuf wanda sakataren gwamnatin jihar Ibrahim Farouk ya wakilta, ya bayyana taron a matsayin wani babban ci gaba a kokarin gwamnatinsa na mayar da jihar Kano a matsayin mai ci gaba a harkokin tafiyar da yanayi da muhalli.

 

Gwamna Yusuf ya jadadda cewa, manufar tana cike da shirin aiwatar da sauyin yanayi, wanda ke fassara kudirin siyasar gwamnati zuwa tsarin aiwatarwa a aikace.

 

 

Ya kuma yi tsokaci kan shirye-shiryen da gwamnati ke yi na samar da makamashi ta hasken rana da ababen more rayuwa.

 

 

Gwamnan ya nanata shirin gwamnatin sa na dasa itatuwa miliyan 5 a shekarar 2025 domin rage zaizaiyar kasa, da inganta iskan shaka, da inganta kyawawan birane.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau
  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16