Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi Allah wadai da zaluncin ‘yan sahayoniyya a kan kasar Yemen

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi kakkausar suka kan harin wuce gona da iri da sojojin yahudawan sahayoniyya suka kai tashar jiragen ruwa na Hodeidah da sauran ababen more rayuwa na kasar Yemen, yana mai bayyana hakan a matsayin babban laifi da kuma keta ka’idoji da dokokin kasa da kasa.

A cikin bayaninsa da sanyin safiyar yau Talata, Baqa’i ya yi nuni da cewa: Hare-haren da ‘yan sahayoniyya suka kai kan tashar jiragen ruwa, da masana’antu, da kuma wuraren zama a kasar Yemen, ana aiwatar da su ne tare da goyon baya da kuma taimakon Amurka. Ya bayyana wadannan hare-haren a matsayin cin zarafi ga doka da kuma keta ka’idoji Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya dangane da mutunta ‘yancin kai na kasa da kuma iyakokin kasa. Ya kuma yi kira da a hada kai da daukar kwararan matakai na kasa da kasa da kasashen yankin don dakile kashe-kashe da barna da Amurka da yahudawan sahayoniyya suke yi a kasashen musulmi.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya jaddada cewa: Hanya daya tilo ta hana yaduwar rashin tsaro a yankin ita ce dakatar da kisan kiyashi da laifuffukan da yahudawan sahayoniyya suke yi a Gaza da kuma kawo karshen rashin hukunta masu aikata muggan laifukan a yankin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

Da take aiwatar da rahotannin sirri cikin gaggawa, rundunar hadin gwiwa da ta kunshi jami’an ‘yansandan Nijeriya, Sojoji, jami’an kula da jama’a na jihar, da ’yan banga na yankin sun bi sawun barayin da suka tsere zuwa Dutsen Falale da ke yankin Kurfi-Safana inda aka yi musayar wuta mai tsanani, wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan bindigar 12.

 

Sai dai kuma, yayin da yake yabawa wannan bajinta da jajircewa da jami’an tsaron suka yi, Dakta Mua’zu ya bayyana matukar alhininsa game da rasuwar wani dan banga mai suna Alhaji Danmalam wanda ya rasa ransa a fafatawar.

 

Bugu da kari, soja guda ya samu raunuka kuma a halin yanzu yana samun kulawa a Asibiti.

 

Alhaji Danmalam ya rasu ne sakamakon harbin bindiga a cibiyar kiwon lafiya ta matakin farko da ke Charanchi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara
  • An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
  • Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
  • Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti 
  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama