Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da “Bankasar tattalin arzikin Iran duk tare da takunkuman tattalin arziki masu tsanani wadanda kasashen yamma musamman Amurka suka doramata, wanda ni tahir amin zan karanta.

////…A dai-dai lokacinda gwamnatin kasar Amurka take barazanar zata hana sayan danyen man fetur daga kasar Iran kwatakwata, sannan take barazanar zata farwa kasar da yaki saboda shirin na makamashin nukliya, sabbin rahotanni sun bayyana cewa iran tana gaba a fitar da kayaki kasuwanci zuwa kasar China sannan ita ce ta 9 a duniya wajen samar da kwan kaji da sauran tsuntsaye.

Kamfanin dillancin labaran Parstoday na kasar Iran ya bayyana cewa, yawan danyen man fetur wanda kasar Iran take sayarwa kasar China kadai  ya kai ganga miliyon 1.8 a ko wace rana a cikin watan Mayun da ya gabata na wannan shekara ta 2025.

Labarin ya kara da cewa kasar Iran a halin yanzu tana sayarwa kasashe 110 kayakin abinci na halal, wadanda suka hana da nama da sauran kayakin abincin na dabbobi. Kuma ita ce kasa ta 9 a duniya wajen samar da kwan suntsaye.

A wani labarin kuma yankin ciniki mara shinge na Aras ya samar da kudaden shiga ga kasar wanda ya kai dalar Amurka miliyon $200 a shekara ta 2024 da ta gabata. Hadi Moghaddamzadeh, shugaban yankin ya bayyana cewa yankin nasa ya samar da kudaden shiga hard alar Amurka miliyon 200, a arewa maso yammacin kasar kuma kudaden shigan da aka samu daga kasar Azerbaijan kadai ya kai dalar Amurka miliyon 11.

A lokacinda yake magana da kamfanin dillancin labaran Pars today a gefen kasuwar baje koli na Iran Expo 2025 wanda aka gudanar a nan Tehran Moghaddamzadeh ya kara da cewa yankin ciniki mara shingen na Aras ya fi muhimmanci a kan sauran iran wannan yankunan da ake da su a nan kasar Iran, saboda wuraren yawon bude ido da shakatawa da yankin yake da su.

A bangaren sayar da kayakin abinci wanda ake kira Halal kuma, shi ne kayakin da iran take fitarwa zuwa kashe kimani 110 a duniya, kuma yake gaza da wasu kasashe a wannan bangaren.

Darakta mai kula da wannan bangaren, ya ce kayakin abinci na Halal wadanda suke fita daga kasar Iran suna zuwa kasashen kamar Malaysia, Singapore, kasashen yankin tekun farisa, arewacin Africa da sauransu.

Ya ce a yankin dai kayakin abinci daga Iran suna shiga kasashen Iraq, Turkiyya, UAE, Afghanistan, Russia, da wasu kasashen Turai.

Sannan shugaban kwastom na Jolfa, ya bayyana cewa a watan da ya gabata, kayakin abince na kimani dalar Amurka miliyon 8.5 suka fita da kofar fitar da kayaki kasuwanci a yankinsa a watan da ya gabata kadai.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kayakin abinci bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Wakilin Hukumar FAO A Iran Yace Sauyin Yanayi Ya shafi Dukkan Yankin

Wakilin hukumar abinci na noma ta duniya FAO,  Farrukh Toirov, ya bayyana cewa sauyin yanayi ya shafi dukkan kasashen yankin Asiya da kudu, don haka yana daga cikin ayyukansu su samar da sabbin dabarbanun ayyukan noma tare da kasar Iran. Sannan JMI a matsayin kasa wacce take tsakiyar kasashen yankin tana iya aika da wadan nan dabarbaru ga sauran kasashen yankin.

Kamfanin dillancin labaran Iran Press ko IP na kasar Iran ya nakalto Farrukh Toirov yana fadar haka, a dai-dai lokacinda ya mika takardun kama aiki a nan Tehran, daga babban cibiyarsu a MDD.

Sabon wakili FAO a Iran ya kammala da cewa hukumarsa zata yi aiki tare da makarantu da cibiyoyin ayyukan noma don aiki tare da kuma samun nasarar kaiwa ga natija mai kyau wajen shawo kan sauyin yanai a kasar da kuma yankin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Malamai A Najeriya Suna Goyon Bayan Iran A Yadda Take Fuskantar HKI August 4, 2025 Shugaban Kasar Lebanon Ya Yi Alkawalin Adalci Ga Wadanda Feshewar Beirut Ta Sha August 4, 2025 Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu August 4, 2025 Pezeshkian ya yaba da irin goyon bayan da Pakistan ta baiwa Iran a lokacin yaki August 4, 2025 Bloomberg: FBI ta cire sunan Trump daga Fayilolin badakalar Epstein August 4, 2025 Jerin gwanon nuna goyon baya ga al’ummar Gaza a Sydney Australia August 4, 2025 MDD ta yi gargadi  game da mummunar matsalar da yunwa ka iya haifarwa ga al’ummar Gaza August 4, 2025 Rasha da China sun fara wani gagarumin atisayen soji na hadin gwiwa a tekun Japan August 4, 2025 Araqchi Ya Bayyana Makomar Sinadarin Uranium Da Iran Ta Inganta A Lokacin Yaki August 3, 2025 Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci  Sun Bayyana Cewa: Masu Shirin Halaka Gaza Suna Son Mamaye Duniyar Musulmi Ne August 3, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Ta Karɓi Rahoton Binciken Kwamishinan Sufuri Kan Belin Wanda Ake Zargi Da Safarar Kwayoyi
  • Wakilin Hukumar FAO A Iran Yace Sauyin Yanayi Ya shafi Dukkan Yankin
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
  • IRGC Tace Bata Amince Da Kasashen Biyu A Kan Kasar Falasdinu Ba
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
  • Pezeskkian Ya Ce: Suna Fatan Musayar Kasuwancin Tsakanin Iran Da Pakistan Ta Haura Dala Biliyan 10
  • Araqchi: Abokantaka Da Ke Tsakanin Iran Da Pakistan Wata babbar Jari Ce Nan Gaba
  • Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
  • Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba