Sharhin bayan Labarai: Ci Gaban Harkokin Kasuwanci Tsakanin Iran Da Kasashen Waje Duk Tare Da Takunkuman Kasashen Yamma
Published: 5th, May 2025 GMT
Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da “Bankasar tattalin arzikin Iran duk tare da takunkuman tattalin arziki masu tsanani wadanda kasashen yamma musamman Amurka suka doramata, wanda ni tahir amin zan karanta.
////…A dai-dai lokacinda gwamnatin kasar Amurka take barazanar zata hana sayan danyen man fetur daga kasar Iran kwatakwata, sannan take barazanar zata farwa kasar da yaki saboda shirin na makamashin nukliya, sabbin rahotanni sun bayyana cewa iran tana gaba a fitar da kayaki kasuwanci zuwa kasar China sannan ita ce ta 9 a duniya wajen samar da kwan kaji da sauran tsuntsaye.
Kamfanin dillancin labaran Parstoday na kasar Iran ya bayyana cewa, yawan danyen man fetur wanda kasar Iran take sayarwa kasar China kadai ya kai ganga miliyon 1.8 a ko wace rana a cikin watan Mayun da ya gabata na wannan shekara ta 2025.
Labarin ya kara da cewa kasar Iran a halin yanzu tana sayarwa kasashe 110 kayakin abinci na halal, wadanda suka hana da nama da sauran kayakin abincin na dabbobi. Kuma ita ce kasa ta 9 a duniya wajen samar da kwan suntsaye.
A wani labarin kuma yankin ciniki mara shinge na Aras ya samar da kudaden shiga ga kasar wanda ya kai dalar Amurka miliyon $200 a shekara ta 2024 da ta gabata. Hadi Moghaddamzadeh, shugaban yankin ya bayyana cewa yankin nasa ya samar da kudaden shiga hard alar Amurka miliyon 200, a arewa maso yammacin kasar kuma kudaden shigan da aka samu daga kasar Azerbaijan kadai ya kai dalar Amurka miliyon 11.
A lokacinda yake magana da kamfanin dillancin labaran Pars today a gefen kasuwar baje koli na Iran Expo 2025 wanda aka gudanar a nan Tehran Moghaddamzadeh ya kara da cewa yankin ciniki mara shingen na Aras ya fi muhimmanci a kan sauran iran wannan yankunan da ake da su a nan kasar Iran, saboda wuraren yawon bude ido da shakatawa da yankin yake da su.
A bangaren sayar da kayakin abinci wanda ake kira Halal kuma, shi ne kayakin da iran take fitarwa zuwa kashe kimani 110 a duniya, kuma yake gaza da wasu kasashe a wannan bangaren.
Darakta mai kula da wannan bangaren, ya ce kayakin abinci na Halal wadanda suke fita daga kasar Iran suna zuwa kasashen kamar Malaysia, Singapore, kasashen yankin tekun farisa, arewacin Africa da sauransu.
Ya ce a yankin dai kayakin abinci daga Iran suna shiga kasashen Iraq, Turkiyya, UAE, Afghanistan, Russia, da wasu kasashen Turai.
Sannan shugaban kwastom na Jolfa, ya bayyana cewa a watan da ya gabata, kayakin abince na kimani dalar Amurka miliyon 8.5 suka fita da kofar fitar da kayaki kasuwanci a yankinsa a watan da ya gabata kadai.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kayakin abinci bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wani Hari Da Zata Fuskanta Daga Makiya
Ministan Tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Za su mayar da martani mai tsanani da karfi kan duk wani ta’addanci da kasarsu za ta fuskanta
Ministan tsaron kasar Iran Birgediya Janar Aziz Nasirzadeh, yayin da yake mayar da martani ga barazanar Amurka, ya tabbatar da cewa Iran za ta mayar da martani mai karfi tare da kai hare-hare kan dukkanin wasu muradun Amurka da sansanoninta da suke wannan yankin.
Birgediya Janar Nasirzadeh ya kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da tarin makamai masu linzami, kuma idan aka kakaba mata yaki, to za ta yi amfani da su ba tare da bata lokaci ba, ko kuma a duk kan muradun makiya.
Ministan ya jaddada cewa: “Ba su da wata kiyayya da kasashe makwabta, amma tabbas idan sansanonin Amurka suka kai hari kan Iran, to lallai muradintaa duk inda suke zasu fuskancin hare-haren daukan fansa,” yana mai cewa: Makami mai linzami na Qasem Basir yana da juriya a fagen yakin na’ura mai kwakwalwa kuma yana iya ketare tsarin makamai masu linzami.”
Ya bayyana cewa: “makamin na Qasem Basir yana da saukin sarrafawa tare da cimma wurin da aka harba shi a kowane yanayi saboda sabon tsarin ci gaban da ya samu da kuma yadda aka sarrafa jikin sa da sinadarin carbon fiber, wanda ke kubuta daga makamai masu linzami da na’urorin radar.”