Jamhuriayar Musulunci ta Iran ta sha alwashin mayar da martani cikin gaggawa ga duk wani kasadan ‘yan Sahayoniyya da Amurka kan kasarta

Jakada kuma zaunannen wakilin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya Amir Sa’ed Irawani ya jaddada cewa: Duk wani kasadan harin soji da Amurka ko wakilliyarta gwamnatin ‘yan  sahayoniyya suke yi, ko da kuwa wani mataki ne da ya sabawa ‘yancin kai, ko cikakken amincin Iran ko kuma muhimman muradun kasa na Jamhuriyar Musulunci ta Iran, za a mayar da martani cikin gaggawa, da ya dace kuma halastacce.

Wannan dai ya zo ne a cikin wata wasika da Amir Sa’ed Irawani, jakada kuma wakilin din-din-din na Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya, ya aikewa babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya António Guterres da shugaban kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya Evangelos C. Sirri dangane da barazana da zargin da fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya yi kan Iran.

Irawani ya kuma jaddada cewa: Zai so ya janwo hankali shugabannin Majalisar Dinkin Duniya da kuma hankalin mambobin kwamitin sulhun Majalisar zuwa ga wani gagarumin keta dokokin kasa da kasa da yahudawan sahayoniya suke yi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Jamhuriyar Musulunci ta Iran Majalisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Yin Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Sahayoniyya Kan Kasar Yemen
  • Iran Ta Mayar Da Martani Akan Zarginta Dangane Da Yemen
  • Iran Ta Jaddada Cewa: Kungiyoyin Gwagwarmaya Ba Su Karbar Umarni Daga Wani Bangare, Gashin Kansu Suke Ci
  • Kasar Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wani Hari Da Zata Fuskanta Daga Makiya
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Ce Masifar Yunwa Ta Kara Yin Kamari A Yankin Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani
  • Wani harin makami mai linzami daga Yemen ya fada filin jirgin saman Ben Gurion na Isra’ila
  • Kasar Yemen Ta Kakaba Takunkumi Kan Amurka A harkokin Fitar Da Man Fetur Din Kasarta
  • ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe