Jamhuriayar Musulunci ta Iran ta sha alwashin mayar da martani cikin gaggawa ga duk wani kasadan ‘yan Sahayoniyya da Amurka kan kasarta

Jakada kuma zaunannen wakilin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya Amir Sa’ed Irawani ya jaddada cewa: Duk wani kasadan harin soji da Amurka ko wakilliyarta gwamnatin ‘yan  sahayoniyya suke yi, ko da kuwa wani mataki ne da ya sabawa ‘yancin kai, ko cikakken amincin Iran ko kuma muhimman muradun kasa na Jamhuriyar Musulunci ta Iran, za a mayar da martani cikin gaggawa, da ya dace kuma halastacce.

Wannan dai ya zo ne a cikin wata wasika da Amir Sa’ed Irawani, jakada kuma wakilin din-din-din na Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya, ya aikewa babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya António Guterres da shugaban kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya Evangelos C. Sirri dangane da barazana da zargin da fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya yi kan Iran.

Irawani ya kuma jaddada cewa: Zai so ya janwo hankali shugabannin Majalisar Dinkin Duniya da kuma hankalin mambobin kwamitin sulhun Majalisar zuwa ga wani gagarumin keta dokokin kasa da kasa da yahudawan sahayoniya suke yi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Jamhuriyar Musulunci ta Iran Majalisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

A ƙalla mutane 15 ne suka mutu sakamakon sabon harin da ‘yan bindiga suka kai a daren Alhamis a ƙauyukan Manja a Mangu da Tangur a ƙaramar hukumar Bokkos, Jihar Filato. An kai harin ne a lokuta daban-daban, inda aka ce Manja aka fara kai hari kafin daga bisani aka farmaki Tangur da misalin ƙarfe 9 na dare.

Majiyoyi sun bayyana cewa maharan sun shigo ƙauyukan suna harbe-harbe ba tare da kakkautawa ba, sannan suka ɓalle gidaje suna kai hari. A cewar majiyar da ke cikin Mangu, mutane bakwai aka kashe a yankin, yayin da mutane takwas suka mutu a Bokkos.

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

Shohotden Mathias Ibrahim, Daraktan Al’adu na ƙungiyar ci gaban Mwaghavul kuma Darakta a sansanin ‘yan gudun hijira da ke Mangu, ya tabbatar da alƙaluman mace-macen a yankin Mangu. Ya bayyana cewa akwai matsanancin tashin hankali a cikin al’umma sakamakon harin.

Sai dai ƙoƙarin da wakilin Daily Trust ya yi na jin ta bakin wasu shugabanni da mazauna Bokkos bai yi nasara ba, yayin da kakakin ‘yansandan Jihar Filato, Alfred Alabo, bai amsa kiran waya da sakonni ba har zuwa lokacin haɗa rahoton nan da safe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom
  • Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu
  • Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
  • “Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
  • An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna
  • Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu
  • Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
  • Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe