Amurka sake kai sabon hari kan kasar Yemen
Published: 5th, May 2025 GMT
Amurka na kara kai hare-hare ta sama a yankuna daban-daban na kasar Yemen.
Babban birnin kasar, Sanaa, shi ne Amurka ta kai wa hari a safiyar yau Litinin.
Wasu hare-hare ta sama da Amurka ta kai a yankunan Bani Matar, Bani Hushaysh da Bani Al-Harith a birnin Sanaa.
Hakazalika, harin da jiragen yakin Amurka suka kai kan wata kasuwa da ke gundumar Shu’ab ta birnin San’a ya lalata shaguna da dama.
A cewar ma’aikatar lafiya ta Yemen, wasu ‘yan kasar 14 ne suka jikkata sakamakon harin da Amurka ta kai a yankin kasuwanci.
Garin Saada da ke arewa maso yammacin kasar, shi ma ya fuskanci hare-hare uku na Amurka.
Bugu da kari, wasu hare-hare ta sama na Amurka sun auna yankuna biyu na yankunan Maarib da al-Jawf na kasar Yemen.
Kakakin Kwamitin Tsaron Amurka James Hewitt, ya ce sojojin Amurka sun kai hare-hare sama da 1,000 a kan Yeman kuma za su ci gaba da kai hare-hare tare da hada kai da Isra’ila.
Hare-haren dai ya biyo bayan nasarar harba makami mai linzami da Yeman ta kai kan yankunan falasdinawa da aka mamaye, wanda ya afkawa filin jirgin sama na Ben Gurion da ke Tel Aviv, lamarin da ya janyo tsaikon zirga-zirgar jiragen sama.
Mutane 8 ne suka jikkata a cewar ma’aikatan jinya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: hare hare ta
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Yau Jumma’a, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum.
Dangane da sanarwar da Amurka ta fitar ta kakaba takunkumi kan jami’an hukumar kare hakkin Falasdinawa da mambobin kungiyar ‘yantar da Falasdinu, Guo Jiakun ya bayyana cewa, Sin ta kadu da hakan, kuma tana nuna takaici da rashin fahimta cewa, Amurka ta yi watsi da kokarin da kasashen duniya ke yi na samar da zaman lafiya ga Falasdinu. Kuma kasar Sin ta dage wajen goyon bayan tsari mai adalci ta al’ummar Falasdinu don maido da halastaccen hakkin al’ummar, kuma za ta ci gaba da yin namijin kokari a wannan fanni tare da sauran kasashen duniya.
Dangane da umarnin da shugaban Amurka Trump ya bayar na kara haraji kan kasashen duniya, Guo Jiakun ya bayyana cewa, matsayin kasar Sin na adawa da cin zarafi na kudaden haraji ba zai canza ba, domin babu wanda zai yi nasara a yakin haraji, kuma ra’ayin amfani da kariyar cinikayya yana cutar da muradun kowane bangare.
Dangane da rahotannin da ke nuni da cewa Amurka ta kaddamar da hare-hare ta yanar gizo kan kasar Sin, Guo Jiakun ya ce, wannan ya fallasa munafuncin Amurkan na koken “kama barawo” a fannin tsaron intanet. Kuma kasar Sin za ta ci gaba da daukar matakan da suka dace don kare tsaron intanet.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp