HausaTv:
2025-06-20@10:29:45 GMT

Amurka sake kai sabon hari kan kasar Yemen

Published: 5th, May 2025 GMT

Amurka na kara kai hare-hare ta sama a yankuna daban-daban na kasar Yemen.

Babban birnin kasar, Sanaa, shi ne Amurka ta kai wa hari a safiyar yau Litinin.

Wasu hare-hare ta sama da Amurka ta kai a yankunan Bani Matar, Bani Hushaysh da Bani Al-Harith a birnin Sanaa.

Hakazalika, harin da jiragen yakin Amurka suka kai kan wata kasuwa da ke gundumar Shu’ab ta birnin San’a ya lalata shaguna da dama.

A cewar ma’aikatar lafiya ta Yemen, wasu ‘yan kasar 14 ne suka jikkata sakamakon harin da Amurka ta kai a yankin kasuwanci.

Garin Saada da ke arewa maso yammacin kasar, shi ma ya fuskanci hare-hare uku na Amurka.

Bugu da kari, wasu hare-hare ta sama na Amurka sun auna yankuna biyu na yankunan Maarib da al-Jawf na kasar Yemen.

Kakakin Kwamitin Tsaron Amurka James Hewitt, ya ce sojojin Amurka sun kai hare-hare sama da 1,000 a kan Yeman kuma za su ci gaba da kai hare-hare tare da hada kai da Isra’ila.

Hare-haren dai ya biyo bayan nasarar harba makami mai linzami da Yeman ta kai kan yankunan falasdinawa da aka mamaye, wanda ya afkawa filin jirgin sama na Ben Gurion da ke Tel Aviv, lamarin da ya janyo tsaikon zirga-zirgar jiragen sama.

Mutane 8 ne suka jikkata a cewar ma’aikatan jinya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hare hare ta

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi

A ci gaba da yakin da suke yi da ’yan ta’adda, sojojin Najeriya sun samu nasarar jikkata jagoran kungiyar ISWAP, Abu Moussab Albarnawi a dajin Sambisa.

Bayanai sun nuna sojoji sun sami nasarar ce bayan wani gagarumin harin da suka kai ta sama a wani sabon sansani na ’yan ta’addan da ke dajin Baikee a yankin Sambisa a Jihar Borno.

Dakarun rundunar da ke karkashin Operation KALACHEN WUTA, wanda bangare ne na rundunar sojojin saman Najeriya da ke karkashin rundunar Operation Hadin Kai (OPHK) ne suka kai harin.

Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu

Majiyoyin sojojin Najeriya da ke rundunar OPHK wanda Manjo Janar Abdulsalam Abubakar ke jagorantar ta ce an aiwatar da wannan aiki ne a dajin inda ’yan ta’addan suke ci gaba da taruwa a sabon sansanin da suka kafa tare da shirya kai hare-hare kan fararen hula da ke kusa, musamman garin Izge.

Majiyar ta ce wannan aikin da Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, Kwamandan Rundunar hadin gwiwa ta Arewa maso Gabas a Operation Hadin ke jagoranta, da kuma kwamandan rundunar sojin sama, kwamanda UU Idris, suka shirya a ranar 13 ga watan Yuni 2025 a jere, yadda aka kai hare-hare da dama kan wuraren taruwar ’yan ta’addan, tare da lalata wasu manyan kadarori da kuma kashe manyan kwamandodi na kungiyar ta ISWAP

Kididdigar barnar da majiyoyi suka tabbatar an yi a harin ta tabbatar da cewa kungiyar ta yi mummunar asara.

Wasu majiyoyin leken asiri sun kara tabbatar da cewa fitaccen shugaban kungiyar ISWAP, Abu Moussab Albarnawi, ya samu munanan raunuka a fuskarsa yayin harin ta sama, duk da cewar har yanzu ba a tabbatar da matsayin raunin da ya ji ba.

Nasarar kawar da ’yan ta’addan da kuma wargaza yunkurinsu na sake haduwa ya rage musu karfin fada sannan ya jefa su cikin rudani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu
  • Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos
  • Guguwar ruwan sama ta yi ɓarna a Kwalejin Kimiyya da Fasaha a Kogi
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • ’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina
  • Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
  • Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
  • “Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki
  • Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi
  • Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila