Amurka sake kai sabon hari kan kasar Yemen
Published: 5th, May 2025 GMT
Amurka na kara kai hare-hare ta sama a yankuna daban-daban na kasar Yemen.
Babban birnin kasar, Sanaa, shi ne Amurka ta kai wa hari a safiyar yau Litinin.
Wasu hare-hare ta sama da Amurka ta kai a yankunan Bani Matar, Bani Hushaysh da Bani Al-Harith a birnin Sanaa.
Hakazalika, harin da jiragen yakin Amurka suka kai kan wata kasuwa da ke gundumar Shu’ab ta birnin San’a ya lalata shaguna da dama.
A cewar ma’aikatar lafiya ta Yemen, wasu ‘yan kasar 14 ne suka jikkata sakamakon harin da Amurka ta kai a yankin kasuwanci.
Garin Saada da ke arewa maso yammacin kasar, shi ma ya fuskanci hare-hare uku na Amurka.
Bugu da kari, wasu hare-hare ta sama na Amurka sun auna yankuna biyu na yankunan Maarib da al-Jawf na kasar Yemen.
Kakakin Kwamitin Tsaron Amurka James Hewitt, ya ce sojojin Amurka sun kai hare-hare sama da 1,000 a kan Yeman kuma za su ci gaba da kai hare-hare tare da hada kai da Isra’ila.
Hare-haren dai ya biyo bayan nasarar harba makami mai linzami da Yeman ta kai kan yankunan falasdinawa da aka mamaye, wanda ya afkawa filin jirgin sama na Ben Gurion da ke Tel Aviv, lamarin da ya janyo tsaikon zirga-zirgar jiragen sama.
Mutane 8 ne suka jikkata a cewar ma’aikatan jinya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: hare hare ta
এছাড়াও পড়ুন:
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp