Ana gwabza kazamin fada a Sudan, inda dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces suka kashe fararen hula kusan 300

A tsakiyar bala’in Sudan, ana ci gaba da gwabza kazamin fada tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa, a daidai lokacin da ake fama da munanan ayyukan jin kai da ke ba da mummunan hoto kan makomar kasar.

A yammacin jihar Kordofan, sojojin kasar Sudan sun sanar da janyewa daga birnin Nahud, bayan kazamin fada da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces, wadanda suka sanar da kwace iko da birnin da kuma hedikwatar Brigade ta sha takwas, baya ga birnin Al-Khawi.

Yayin da ake ci gaba da gwabza fada, gwamnatin Sudan ta zargi dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces da aikata munanan laifuka kan fararen hula a birnin Nahud, da suka hada da kisan kai, sace-sacen dukiya da lalata cibiyoyi. Ta kuma sha alwashin hukunta wadanda ke da hannu a aikata wadannan muggan laifuka da kuma kasashen da ke tallafa musu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: dakarun kai daukin gaggawa

এছাড়াও পড়ুন:

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

A yau Asabar, hukumar bayar da agajin gaggawa ta birnin Beijing ta sanar da cewa, an dawo da wutar lantarki da ayyukan sadarwa a dukkan kauyukan da ibtila’i ya shafa a fadin birnin na Beijing, biyo bayan mamakon ruwan sama da iska mai karfi da aka tafka, yayin da kuma ake ci gaba da aikin ceto wadanda suka bace.

Ruwan sama da iska mai karfi da aka yi fama da shi daga ranar 23 zuwa 29 ga watan Yuli ya yi sanadin mutuwar mutane 44, yayin da mutane tara suka bace, a babban birnin kasar, kamar yadda aka sanar a wani taron manema labarai da aka gudanar a ranar Alhamis da ta gabata.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta birnin ta ce, zuwa safiyar yau Asabar, an magance matsalar samar da ruwan sha a yankunan da bala’in ya shafa.

Ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka tafka a yankunan tsaunuka na arewaci, ya haifar da lalacewar kayayyakin more rayuwa a garuruwa 40 da kauyuka 312, lamarin da ya shafi fiye da mazauna yankunan 300,000 tare da lalata gidaje kusan 24,000. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing
  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • ‘Yan Sudan dama na komawa gida bayan gudun hijira na tsawon shekaru a Masar
  • Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing
  •  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
  • Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku