Ana gwabza kazamin fada a Sudan, inda dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces suka kashe fararen hula kusan 300

A tsakiyar bala’in Sudan, ana ci gaba da gwabza kazamin fada tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa, a daidai lokacin da ake fama da munanan ayyukan jin kai da ke ba da mummunan hoto kan makomar kasar.

A yammacin jihar Kordofan, sojojin kasar Sudan sun sanar da janyewa daga birnin Nahud, bayan kazamin fada da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces, wadanda suka sanar da kwace iko da birnin da kuma hedikwatar Brigade ta sha takwas, baya ga birnin Al-Khawi.

Yayin da ake ci gaba da gwabza fada, gwamnatin Sudan ta zargi dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces da aikata munanan laifuka kan fararen hula a birnin Nahud, da suka hada da kisan kai, sace-sacen dukiya da lalata cibiyoyi. Ta kuma sha alwashin hukunta wadanda ke da hannu a aikata wadannan muggan laifuka da kuma kasashen da ke tallafa musu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: dakarun kai daukin gaggawa

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatan Da Ba Malamai Ba A Jami’ar Jihar Taraba Sun Fada Yajin Aiki

Shugaban Kungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’o’in Najeriya (SSANU), Comr. Muhammad Haruna Ibrahim ya bukaci gwamnatin jihar Taraba da ta gaggauta biyan ‘yan kungiyar SSANU, jami’ar Jalingo ta jihar Taraba alawus-alawus da suke bi bashi.

 

Comr. Haruna ya yi wannan bukata ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron majalisar zartarwa na shiyyar karo na 11 da ya gudana a Jalingo.

 

Shugaban SSANU ya dage cewa ya kamata a yi wa ’ya’yan kungiyar adalci, domin wadanda ba aikin koyarwa ba na daga cikin bangarori hudu da suka kafa jami’a.

 

Sai dai ya yi gargadin cewa kungiyar ba za ta goyi bayan duk wani memba da ya sabawa ka’idojin jami’a ba.

 

Tun da farko, Comr. Bitrus Joseph Ajibauka, shugaban kungiyar TSU reshen, ya yabawa gwamna Agbu Kefas bisa yadda ya amince da biyan wani bangare na bashin albashi da alawus-alawus na kungiyar da kuma aiwatar da sabon mafi karancin albashi na N70,000.

 

JAMILA ABBA

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Hizbullahi Ta Lebanon Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Suka Kai Kan Kasar Siriya
  •  Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-haren HKI Akan Syria Da Nufin Rusa Kasar
  • Kotu Ta Daure Wasu Mutum Biyu Da Suka Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 14 Fyade A Birnin Kebbi
  • Yadda sojoji suka kashe manyan ’yan bindiga 5 a Zamfara
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Kakkausar Suka Kan Hare-Haren Jiragen Saman Amurka Kan Kasar Yemen
  • Jiragen Saman Yakin Sojojin Isra’ila Sun Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Siriya
  • Ma’aikatan Da Ba Malamai Ba A Jami’ar Jihar Taraba Sun Fada Yajin Aiki
  • Rikicin Boko Haram Da ISWAP: An Kashe Masunta 18, Mutane  Da Yawa Sun Bace
  • Gwamnatin Kano Zata Kashe Naira Miliyan Dubu 51 Don Aiwatar Da Ayukka