Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Matsin Lamba Kan Iran Ba Zai Yi Tasiri Ba
Published: 5th, February 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Tsananta matsin lamba da ake son dauka kan Iran ba zai yi wani tasiri ba
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Manufar matsin lamba da shugaban Amurka Donald Trump ya dauka kan Iran za ta sake yin kasa a gwiwa tare da rashin nasara.
Araqchi ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar bayan kammala zaman majalisar ministocin a yau Laraba, inda ya ce mafi girman matsin lamba shi ne gwajin da aka yi kan kasar Iran da bai yi nasara ba, ya kara da cewa; Idan babban batu shi ne cewa Iran ba ta kama hanyar mallakar makamin nukiliya ba, to hakan na iya yiwuwa kuma babu wata matsala a wannan bangaren.
Araqchi ya jaddada cewa: Matsayin Iran a bayyane yake, kuma ita mamba ce ta NPT (yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya) kuma fatawar Jagoran juyin juya halin Musulunci tana da inganci da kuma bayyana irin nauyin da ke wuyan kasar ta Iran.
Shugaban Amurka Donald Trump ya fada a yammacin jiya Talata bayan sanya hannu kan wata doka mai dawo da manufar matsin lambar siyasa kan kasar Iran cewa: Za su kakaba wa Iran “takunkumi mai tsanani” tare da dakatar da fitar da man da take fitarwa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana a yau Litinin cewa, babu wata tattaunawa da aka yi ta wayar tarho tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka a baya-baya nan, haka kuma bangarorin biyu ba su cimma wata yarjejeniya ko su tuntubi juna game da batun haraji ba. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp