Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Matsin Lamba Kan Iran Ba Zai Yi Tasiri Ba
Published: 5th, February 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Tsananta matsin lamba da ake son dauka kan Iran ba zai yi wani tasiri ba
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Manufar matsin lamba da shugaban Amurka Donald Trump ya dauka kan Iran za ta sake yin kasa a gwiwa tare da rashin nasara.
Araqchi ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar bayan kammala zaman majalisar ministocin a yau Laraba, inda ya ce mafi girman matsin lamba shi ne gwajin da aka yi kan kasar Iran da bai yi nasara ba, ya kara da cewa; Idan babban batu shi ne cewa Iran ba ta kama hanyar mallakar makamin nukiliya ba, to hakan na iya yiwuwa kuma babu wata matsala a wannan bangaren.
Araqchi ya jaddada cewa: Matsayin Iran a bayyane yake, kuma ita mamba ce ta NPT (yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya) kuma fatawar Jagoran juyin juya halin Musulunci tana da inganci da kuma bayyana irin nauyin da ke wuyan kasar ta Iran.
Shugaban Amurka Donald Trump ya fada a yammacin jiya Talata bayan sanya hannu kan wata doka mai dawo da manufar matsin lambar siyasa kan kasar Iran cewa: Za su kakaba wa Iran “takunkumi mai tsanani” tare da dakatar da fitar da man da take fitarwa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
Fitattun dalibai akalla 12 ne daga makarantun gwamnati suka samu guraben tallafin karatun sakandare a ƙarƙashin Asusun Tallafin Karatu na Jihar Kwara (Kwara-ETF).
A wajen taron gabatarwa ga waɗanda suka fara cin moriyar shirin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana cewa ci gaban harkar ilimi a Najeriya abu ne mai tsada kuma ya zama wajibi kowa ya bayar da gudummawarsa.
Ya roƙi masu masu hannu da shuni da kungiyoyi masu zaman kansu da su tallafa wajen gina makarantu ko kuma su ɗauki nauyin daliban da suka nuna bajinta da jajircewa a harkar karatu.
A cewarsa, an zabo daliban 12 ne sakamakon bajintar da suka nuna a matakai daban-daban na tantancewa da Kwara ETF ta gudanar.
Gwamnan ya bayyana cewa tallafin ya kunshi dukkan kuɗin da ake buƙata a karatun sakandaren daliban.
“Muna kira da jama’a su ba da gudummawa da kuma ɗaukar nauyin ɗalibai. Kada a bar wannan aiki ga gwamnati da iyaye kadai. Ilimantar da ‘ya’yanmu hakki ne da ya rataya a kanmu gaba ɗaya,” in ji Gwamna.
Ya yaba da tsarin zaɓen kuma ya taya waɗanda suka yi nasara murna.
A nata jawabin, Babbar Shugabar Kwara ETF, Oluwadamilola Amolegbe, ta ce daliban 12 sun fito ne daga cikin jerin ɗalibai 640 da aka fara tantancewa bisa cancanta.
Ta bayyana cewa tsarin zaɓen ya fara ne da rubuta jarabawa ga dukkan daliban firamare na aji shida da suka amfana da shirin KwaraLEARN na koyon fasahar zamani, har zuwa lokacin da aka kammala tantancewa.
Ali Muhammad Rabi’u