Kasar Iran Ta Bayyana Shirinta Na Mayar Da Martani Ga Duk Wata Barazana Kanta
Published: 5th, February 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Iran za ta mayar da martani ga duk wata barazana ko matsin lamba gwargwadon tsayin dakarta
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana cewa: Iran ta sha tabbatar da cewa a shirye take ta gudanar da huldar siyasa da diflomasiyya don tabbatar da moriyar kasa, kuma tana shirye ta gudanar da kumajin siyasa da diflomasiyya wajen kare muradunta da tsaron kasa, sannan tana da azamar daukan duk wani matakin kare kanta da masalaharta tare da mayar da martani ga duk wata barazana ko matsin lamba gwargwadon tsayin daka da gwagwarmayarta.
Isma’il Baqa’i ya bayyana haka ne a yayin da yake mayar da martani ga tambayar cewa; Maganganun da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi a baya-bayan nan dangane da Iran, inda ya jaddada cewa: Zarge-zargen da ake yi kan Iran cewa tana yunkurin kera makaman kare dangi, kawai da’awar karya ce tsagwaranta. Sannan Iran din ta tabbatar da karce-karyacensu sau da dama, kuma duk wanda ya nemi tabbas kan wannan lamari zai iya samun cikin sauki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF) ta zargi Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da kin yin adalci wurin ayyuka da raba mukamai tsakanin Arewa da Kudancin Kasar nan.
Wadannan zarge-zarge suka sa fadar Shugaban Kasa ta hannun mai taimaka masa na musamman kan kafofin yada labarai Bayo Onanuga mayar da martani ga kungiyar ta ACF.
Ko wadanne irin martani fadar shugaban kasar ta mayar ga kungiyar?
NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aureWannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan