HausaTv:
2025-11-03@08:50:49 GMT

Sojojin Sudan Sun Kwace Birnin Al-Kamlin Da Ke Jihar Aljazira A Tsakiyar Kasar

Published: 5th, February 2025 GMT

Sojojin Sudan sun kwace iko da birnin Al-Kamlin da ke jihar Aljazira a tsakiyar kasar

Rundunar sojin Sudan ta sanar a yau jiya Talata cewa: Sojojinta da mayakan da suke goya musu baya sun kwace iko da birnin Al-Kamlin da ke jihar Aljazira a tsakiyar kasar, kuma babban hafsan hafsoshin rundunar sojin kasar Janar Abdul-Fattah Al-Burhan ya yi alkawarin samun nasara a nan kusa kadan kan wadanda ya kira ‘yan tawaye.

Sojojin Sudan sun watsa labarin ta hanyar kafofin Facebook da Instagram tare da wallafa faifan bidiyon yadda al’ummar birnin suka fito kan tituna suna bayyana murnarsu da ‘yantar da birninsu daga hannun ‘yan tawaye tare da bayyana wannan nasara a matsayin babban ci gaba ga sojojin Sudan.

A nasa bangaren, shugaban majalisar gudanar da mulkin Sudan, kuma babban hafsan hafsoshin sojin kasar Laftanar Janar Abdel Fattah Al-Burhan ya ce: Sojoji na gab da kammala samun nasara bayan da suka fatattaki Dakarun Kai Daukin Gaggawa na Rapid Support Forces a dukkan yankunan birnin Khartoum fadar mulkin kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan

Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi ya gana da Shugaban Eritrea Isaias Afwerki domin tattauna halin da ake ciki a yankin,  Shugaba al-Sisi ya tabbatar da jajircewar Masar wajen tallafawa ‘yancin kai da kuma ‘yancin yankin Eritrea.

A yayin taron, wanda Ministan Harkokin Wajen Masar Badr Abdel-Aty da takwaransa na Eritrea, Osman Saleh Mohammed suka halarta, shugabannin biyu sun tattauna halin da ake ciki a yankin.

Sun tabbatar da hangen nesansu kan hanyoyin kawo karshen yakin a Sudan, suna masu  jaddada bukatar tallafawa cibiyoyin gwamnati na kasa, musamman Sojojin Sudan, tare da kin amincewa da duk wani yunkuri na kafa hukumomi ko cibiyoyi  masu kishiyantar gwamnati a kasar.

Shugaba al-Sisi ya jaddada matsayar Masar da kuma  kokarin da take yi  don kawo karshen yakin da kuma rage wahalhalun jin kai na al’ummar Sudan, ta hanyar yin aiki tare da abokan huldar Masar  don tabbatar da hadin kan Sudan, mutuncin yankin, da kuma ‘yancin kan kasa.

A nasa bangaren, Shugaba Afwerki ya nuna matukar godiyarsa ga rawar da y ace Masar tana  takawa karkashin jagorancin Shugaba El-Sisi, wajen karfafa zaman lafiya da kuma kokarin ci gaban  yankin kusurwar Afirka da Gabashin Afirka. Ya yi maraba da fadada hadin gwiwar tattalin arziki da Masar da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu kan batutuwan kasa da kasa da na yanki masu amfani ga junansu.

Taron ya kuma yi magana kan sabbin abubuwan da suka faru a Somaliya, inda Shugabannin biyu sun jaddada kudurin kasashensu na amincewa da sanarwar hadin gwiwa da aka fitar a taron kolin Masar, Eritrea, da Somaliya a Asmara a watan Oktoban 2014, wanda ya tabbatar da wajibcin girmama ka’idoji da dokokin kasa da kasa, musamman ma cikakken yankin Somaliya da dukkan kasashen yankin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan