Jami’in tsaron kasar Iran ya karyata sabuwar da’awar jaridar New York Times ta kasar Amurka

Jami’in tsaron kasar Iran ya musanta wasu sabbin zarge-zargen da jaridar New York Times ta Amurka ta wallafa game da zargin Iran cewa tana bunkasa ayyukannta na kera makaman kare dangi.

Jami’in tsaron ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Tasnim cewa: Ikirarin da jaridar New York Times ta yi game da wata kungiyar asiri ta masana kimiyyar Iran da ke aikin samar da hanyoyin kera makaman nukiliya cikin sauri, ba komai ba ne illa shirme da zage-zage marasa tushe da kan gado.

Jami’in ya kara da cewa: “Wadannan rudun tunani ba su da alaka da gaskiya, kuma kawai labaran karya ne da wasu kafafen yada labarai na Amurka ke yi don goyon bayan ajandar fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ‘yar mamaya Benjamin Netanyahu.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Amurka Ya Bukaci Amurka Ta Jefa Makaman Nukliya Kan Gaza

Wani dan majalisar dokokin kasar Amurka daga jam’iyyar Republican daga jihar Florida Randi Fine ya bukaci gwamnatin Amurka ta yi amfani da dimbin makaman N uklkiya da ta tara don kawo karshen yaki a gaza, ta kashe dukkan Falasdinawa a lokaci guda a huta.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Fine yana fadar haka a wata hira da ta hadashi da tashar talabijin ta Foxnews a jiya Alhamis.

Ya kuma  kara da cewa Amurka bata shiga tattaunawa da sojojin Nazi a yakin dunbiya na biyu ba, bata kuma yi kome bas ai da ta yi amfani da makaman nuklioya a kan Hiroshima da kuma Nagasafi sai kasar Japan ta mika kai ba tare da wasu matsala ba.

Fine yace a yanzun ma al-amarin ya kai ga zabin amfani da Nukliya kan Gaza kawai ta rage.

Labarin ya kara da cewa wannan bas hi ne karon farko wanda Randy Fine yake kiran gwamnatin Amurka ta yi haka ba. Kuma ya sha suka daga kungiyoyi daban daban.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Donal Trump Ya Kori Gomomi Daga Cikin Ma’aikata A Majalisar Tsaro Ta Kasar Amurka
  • Jonh Kerry Ya Ce HKI Ba Zata Iya Wargaza Cibiyoyin Nukliyar Kasar Iran ba
  • Maariv: Tattaunawa A Tsakanin “Isra’ila” Da Kasashen Afirka Ta Yi Nisa Akan Hijirar Mutanen Gaza
  • Majiyoyin Iran Sun Musanta Da’awar Karya Kan Neman Ziyarar Amurka Zuwa Cibiyoyin Sojojinta
  • Kotu A Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Tsohon Jami’in Kasar Kan Hannu A Kashe-Kashen Rayukan Jama’a
  • Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jaridar Da Ya Fallasa ‘Sharrin’ Da Ake Shirya Wa Natasha
  • Amurka Tana Takurawa JMI Don Biyan Bukatun HKI Na Ta Dakatar Da Shirinta Na Nukliya
  • Iran: Inda Makiya Kasar Sun San Cewa Zasu Sami Nasara A Kan Iran A Yaki Da Tuni Sunn Farmata Da Yaki
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Amurka Ya Bukaci Amurka Ta Jefa Makaman Nukliya Kan Gaza
  •   Ma’ariv: “Isra’ila” Ta Zama Saniyar Ware A Duniya