Meta zai biya Trump $25m kan rufe shafinsa
Published: 30th, January 2025 GMT
Kamfanin Meta, mamallakin Facebook, ya amince zai biya dala miliyan 25 don sasantawa kan shari’ar da Donald Trump, ha shigar game da rufe masa shafinsa.
Trump, ya maka Meta a kotu a shekarar 2021 bayan da Facebook ya rufe shafinsa sakamakon harin da aka kai Majalisar Dokokin Amurka a ranar 6 ga watan Janairu.
Kaso mafi tsoka na kuɗin wanda ya kai dala miliyan 22—zai tafi ne wajen gina ɗakin karatu na Trump, yayin da sauran ƙudin za a biya lauya da wasu mutane da suka shigar da ƙarar tare da shi.
Trump, ya kuma maka Twitter (wanda yanzu ake kira X) da YouTube a kotu saboda rufe shafukansa, amma kotu t kori ƙarar.
A baya, Facebook ya dakatar da Trump saboda yaɗa labaran ƙarya kan zaɓen Amurka na 2020, amma daga baya ta rage takunkumin zuwa shekaru biyu, sannan ta dawo masa da shafukansa a shekarar 2023.
Rahotanni sun ce tattaunawar sulhu ta fara ne a watan Nuwamban 2024 lokacin da Shugaban Kamfanin Meta, Mark Zuckerberg, ya gana da Trump a gidansa na Mar-a-Lago.
Bayan wats tattaunawa da suka yi a watan Janairun 2025, Meta ta amince da cire wasu takunkumai da aka ƙaƙaba wa shafukan Trump.
Trump, wanda shi ne sabon shugaban Amurka, a baya ya yi amfani da shafukansa na sada zumunta wajen jadadda iƙirarin cewar shi ne ya lashe zaɓe 2020 da aka gudanar a ƙasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Mark Zuckerberg
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
Yau Laraba 30 ga wata, an kira taro a ofishin siyasa na kwamitin koli na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (JKS), inda aka yanke shawarar gudanar da cikakken zama na 4 na kwamitin koli na 20 na JKS a watan Oktoba na shekarar da muke ciki, domin nazari kan shawarar tsara shirin shekaru biyar-biyar na bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin na 15.
Taron ya nuna cewa, lokacin gudanar da “Shirin shekaru biyar-biyar din na 15”, lokaci ne mai muhimmanci a fannin tabbatar da ingantaccen tushe, da kokarin raya zamanantar da kasar Sin bisa tsarin gurguzu. A yanzu haka yanayin ci gaban kasar Sin yana fuskantar manyan sauye-sauye masu sarkakiya, akwai kuma damarmaki bisa manyan tsare-tsare da ma kalubale tare.
A waje guda kuma, tattalin arzikin kasar yana da tushe mai karko, da tarin fifiko, da karfin juriya, da kuma makoma mai kyau a nan gaba. Har ila yau, fifikon da kasar Sin ke da shi a fannonin tsarin gurguzu mai halin musamman irin na kasar, da kasuwa mai girma sosai, da cikakken tsarin masana’antu, da kuma albarkatun kwararru, ya fi bayyana sosai.
Taron ya kuma nuna cewa, kamata ya yi a kara azamar cimma nasara, da gudanar da ayyuka yadda ya kamata, don samun rinjaye bisa manyan tsare-tsare a yayin da Sin ke shiga takara a duniya, da ma samun babban ci gaba a ayyukan da suka shafi zamanantarwa irin ta kasar Sin. (Mai fassara: Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp