Aminiya:
2025-06-15@19:33:11 GMT

Meta zai biya Trump $25m kan rufe shafinsa

Published: 30th, January 2025 GMT

Kamfanin Meta, mamallakin Facebook, ya amince zai biya dala miliyan 25 don sasantawa kan shari’ar da Donald Trump, ha shigar game da rufe masa shafinsa.

Trump, ya maka Meta a kotu a shekarar 2021 bayan da Facebook ya rufe shafinsa sakamakon harin da aka kai Majalisar Dokokin Amurka a ranar 6 ga watan Janairu.

Masu ɗibar fetur daga tankar da ta faɗi sun kai wa jami’an kashe gobara hari DR Congo: Sojoji sun ƙaddamar da gagarumin hari kan ’yan tawayen M23 —Shugaba Tshisekedi

Kaso mafi tsoka na kuɗin wanda ya kai dala miliyan 22—zai tafi ne wajen gina ɗakin karatu na Trump, yayin da sauran ƙudin za a biya lauya da wasu mutane da suka shigar da ƙarar tare da shi.

Trump, ya kuma maka Twitter (wanda yanzu ake kira X) da YouTube a kotu saboda rufe shafukansa, amma kotu t kori ƙarar.

A baya, Facebook ya dakatar da Trump saboda yaɗa labaran ƙarya kan zaɓen Amurka na 2020, amma daga baya ta rage takunkumin zuwa shekaru biyu, sannan ta dawo masa da shafukansa a shekarar 2023.

Rahotanni sun ce tattaunawar sulhu ta fara ne a watan Nuwamban 2024 lokacin da Shugaban Kamfanin Meta, Mark Zuckerberg, ya gana da Trump a gidansa na Mar-a-Lago.

Bayan wats tattaunawa da suka yi a watan Janairun 2025, Meta ta amince da cire wasu takunkumai da aka ƙaƙaba wa shafukan Trump.

Trump, wanda shi ne sabon shugaban Amurka, a baya ya yi amfani da shafukansa na sada zumunta wajen jadadda iƙirarin cewar shi ne ya lashe zaɓe 2020 da aka gudanar a ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Mark Zuckerberg

এছাড়াও পড়ুন:

Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci

Jagoran juyin musulunci na Iran wanda shi ne babban kwamandan rundunonin sojan kasar Iran, ya nada sabbin kwamandoji da maye gurbinsu da wadanda su ka yi shahada.

Bayan shahadar kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci Shahid Hussain Salami, da kuma  babban hshahid Muhammad Hussain Bakiri, sai Shahid Gulam Ali Rashid wanda shi ne kwamandan Bakirin soja na “Khatamul-Anbiya, jagoran juyin ya sanar da sunayen wadanda su ka maye gurbinsu.

Birgediya Muhammad Pakphur shi ne wanda jagoran ya sanar a matsayin sabon kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci, sai kuma  Manjo Janar Musawi a mastayin sabon kwamandan rundunar sojan kasar, yayin da aka nada janar Ali Shadmani a matsayin kwamandan Barikin soja na Khatamul-Anbiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Asalin Tudun Loess
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2