Aminiya:
2025-11-03@17:05:38 GMT

Meta zai biya Trump $25m kan rufe shafinsa

Published: 30th, January 2025 GMT

Kamfanin Meta, mamallakin Facebook, ya amince zai biya dala miliyan 25 don sasantawa kan shari’ar da Donald Trump, ha shigar game da rufe masa shafinsa.

Trump, ya maka Meta a kotu a shekarar 2021 bayan da Facebook ya rufe shafinsa sakamakon harin da aka kai Majalisar Dokokin Amurka a ranar 6 ga watan Janairu.

Masu ɗibar fetur daga tankar da ta faɗi sun kai wa jami’an kashe gobara hari DR Congo: Sojoji sun ƙaddamar da gagarumin hari kan ’yan tawayen M23 —Shugaba Tshisekedi

Kaso mafi tsoka na kuɗin wanda ya kai dala miliyan 22—zai tafi ne wajen gina ɗakin karatu na Trump, yayin da sauran ƙudin za a biya lauya da wasu mutane da suka shigar da ƙarar tare da shi.

Trump, ya kuma maka Twitter (wanda yanzu ake kira X) da YouTube a kotu saboda rufe shafukansa, amma kotu t kori ƙarar.

A baya, Facebook ya dakatar da Trump saboda yaɗa labaran ƙarya kan zaɓen Amurka na 2020, amma daga baya ta rage takunkumin zuwa shekaru biyu, sannan ta dawo masa da shafukansa a shekarar 2023.

Rahotanni sun ce tattaunawar sulhu ta fara ne a watan Nuwamban 2024 lokacin da Shugaban Kamfanin Meta, Mark Zuckerberg, ya gana da Trump a gidansa na Mar-a-Lago.

Bayan wats tattaunawa da suka yi a watan Janairun 2025, Meta ta amince da cire wasu takunkumai da aka ƙaƙaba wa shafukan Trump.

Trump, wanda shi ne sabon shugaban Amurka, a baya ya yi amfani da shafukansa na sada zumunta wajen jadadda iƙirarin cewar shi ne ya lashe zaɓe 2020 da aka gudanar a ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Mark Zuckerberg

এছাড়াও পড়ুন:

Trump ya jaddada shirin Amurka na kai hari a Najeriya

Shugaba Donald Trump, ya jaddada cewa Amurka na iya tura sojoji ko ƙaddamar da hare-hare a kan Najeriya idan har kashe-kashen da ya ce ana yi wa Kiristoci suka ci gaba.

A yayin tattaunawa da manema labarai da kuma saƙonnin da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Mista Trump ya ce ba zai zauna yana kallo ba. “Ana kashe Kiristoci da dama a Najeriya; ba zan bari a ci gaba ba,” in ji shi.

A sakon da ya wallafa a dandamalin Truth a ranar Asabar, Trump ya ce Washington na iya shiga Najeriya da ƙarfin soji domin “kakkaɓe” abin da ya kira ƙungiyoyin ƴan ta’adda masu kishin addinin Islama.

Haka kuma ya yi barazanar dakatar da duk wani taimakon Amurka zuwa Najeriya idan wannan har ya ci gaba.

Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato

Wannan batu ya biyo bayan matakin da Amurka ta ɗauka a baya-bayan nan, inda ta saka Najeriya cikin jerin ƙasashen da take nuna damuwa game da take ’yancin addini.

Sai dai fadar gwamnatin Najeriya ta ce za ta yi maraba da duk wani haɗin gwiwa daga Amurka wajen yak6i da masu tsattsauran ra’ayi, amma ta musanta zargin cewa mayakan sun fi kashe Kiristoci kawai.

Hukumomin Najeriya sun jaddada cewa rikice-rikicen tsaro a ƙasar sun shafi duka al’ummomin — Kiristoci da Musulmai — ba tare da bambanci ba.

Tun a ranar Juma’a, Trump ya riƙa wallafa zarge-zargen cewa “ana kashe dubban Kiristoci a Najeriya” kuma masu tsattsauran ra’ayin Islama ne ke aikata hakan — bayanin da bai kawo hujjoji masu ƙarfi ba.

Wani ɓangare na siyasar Amurka ma ya ƙara ƙarfafa wannan muhawara: a watan Maris ɗan majalisar wakilai Chris Smith ya yi kira a saka Najeriya a jerin ƙasashen da ake damuwa da su; yayin da a watan Oktoba Sanata Ted Cruz da ɗan majalisar Riley Moore — dukkansu ’yan Republican ne — suka zargi gwamnatin Najeriya da yin shiru ko yin watsi da batun.

Wannan zargi ya ƙara ƙarfafa masu jaddada cewa ana kashe Kiristoci a Najeriya, tare da sake tada muhawara kan yadda za a magance matsalolin tsaro a ƙasar.

Masana tsaro da dama sun lura cewa Najeriya ta daɗe tana haɗuwa da rikice-rikice daban-daban — na ƙabilanci, na addini da na ‘yan ta’adda — inda mafi yawan raunuka da asarar rai ke faruwa a fannoni daban-daban na al’umma.

Hakan na nuna bukatar a yi nazari mai zurfi kafin ɗaukar matakai masu tsanani irin su tura dakarun ƙasashen waje.

Fadar gwamnatin Najeriya ta ce za ta marabci duk wani taimako daga Amurka wajen yaki da mayaka masu tsattsauran ra’ayi, amma ta musanta zargin cewa mayakan sun fi kashe Kiristoci kaɗai. Hukumomin Najeriya sun jaddada cewa rikice-rikicen tsaro a ƙasar sun shafi kowa — Kiristoci da Musulmai — kuma batun yana buƙatar a duba shi cikin natsuwa.

Mene ne ƙarfin ikon Amurka?

Trump ya jawo hankalin jama’a da cewa a wa’adinsa na farko ya saka Najeriya cikin jerin ƙasashen da take da damuwa da su, amma gwamnatin da ta gaje shi, Joe Biden, ta cire Najeriya daga wannan jerin a 2021.

A kan aiwatar da irin wannan mataki na amfani da soji, masana suna ta muhawara: Kundin Tsarin Mulkin Amurka, sashe na 8, yana ba Majalisar Dokokin Amurka ikon ayyana yaƙi da kuma tsara dokokin da suka shafi mamaye ƙasa da teku.

Sai dai a aikace, kundin ya tanadi cewa majalisar ne ke da ƙarfin yanke shawara mai ƙarfi kan irin matakin da za a ɗauka — wato Shugaban ƙasa ba shi kaɗai zai iya yanke hukunci mai zurfi ba tare da goyon bayan dokokin ƙasa ba.

A bangaren dokokin duniya, Majalisar Ɗinkin Duniya ta jaddada cewa amfani da ƙarfin ƙasa kan wata ƙasa ba abu ne da za a lamunta ba sai dai a cikin yanayin kare kai ko kan wata hujja ta doka da ta amince.

 

Me doka ta ce a kan kutse?

A hira da BBC, Barista Audu Bulama Bukarti, masani kan shari’a da tsaro a Afirka, ya bayyana cewa Amurka ba ta da hurumin kutsawa Najeriya domin yakar ta’addanci sai da izinin Najeriya da kuma tsarin doka na kasa da kasa.

“Amurka ba ta da ikon afka wa Najeriya domin Najeriya ƙasa ce mai zaman kanta wadda take da cikakken ‘yanci,” in ji shi.

Ya ce doka ta kasa da kasa, ciki har da wasu dokoki da bayyanannun ƙa’idojin Majalisar Dinkin Duniya, sun haramta aikata kutse kai tsaye ba tare da izini ba.

A cewar sa, haramun ne ga wata ƙasa ta shigo sararin samaniyar Najeriya ko ta yi kutse cikin ƙasar ba tare da amincewar gwamnati ba.

Makomar muhawara

Duk da zarge-zargen da wasu ’yan siyasa da masu ra’ayin kishin addini a ƙasashen waje suka yi, masana tsaro da lauyoyi na nan suna jaddada cewa duk wani mataki na soja da za a ɗauka a ƙasa ta waje yana buƙatar cikakken bin doka — na cikin gida da na duniya.

Hakan na nuna cewa kafin a ɗauki mataki mai tsanani irin turawa ko amfani da soji, dole ne a yi nazari mai zurfi, a nemi izini daga hukumomin Najeriya, ko a bi hanyoyin doka na ƙasa da ƙasa.

A ƙarshe, gwamnatin Najeriya ta ce za ta amince da taimako na gaskiya daga ƙawance amma ba za ta lamunci wata ƙasa ta yi amfani da ƙarfin soja a kan ƙasar ba sai an bi doka da tsarin da ya dace.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
  • Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 
  • Trump ya jaddada shirin Amurka na kai hari a Najeriya
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3