Aminiya:
2025-06-09@00:01:23 GMT

Queen Zeeshaq za ta shiga daga ciki

Published: 20th, May 2025 GMT

Zainab Ishaq Muhammad, wadda aka fi sani da ‘Queen Zeeshaq’ za ta shiga daga ciki a ranar Lahadi mai zuwa.

Duk da cewa ba a yayata batun auren ba, Aminiya ta tabbatar da ganin katin gayyata da ke nuna za a ɗaura auren nata da angonta, Hussain Muhammad Koya, a ranar 25 ga watan Mayu, 2025.

’Yan sanda sun cafke ’yan fashi 6, sun ƙwato motocin sata 4 a Kano An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato

Rahotanni sun nuna cewar a ranar Laraba za a fara bidirin bikin har zuwa ranar Asabar.

An shirya gudanar da walima, ƙwallon ƙafa, saukar karatun Alƙur’ani da sauransu har zuwa ranar ɗaurin aure.

A yanzu matashiyar ta fi mayar da hankali wajen ayyukan jin-ƙan marayu da kuma aikin jarida.

Aminiya ta tuntuɓi makusantan mawaƙiyar don jin dalilin ɓoye bikin, amma sun ce wasu dalilai ne ya sa suka ɗauki wannan mataki.

Matashiyar ta fice a kafafen sada zumunta musamman Facebook, inda ake yin gwagwarmaya da ita kan harkokin yau da kullum.

Ga katin bikin a ƙasa:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Matashiya Mawaƙiya Waƙoƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu
  • Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki
  • An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya
  • Edgar Lungu: Za a yi zaman makokin kwana 7 a Zambiya 
  • Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
  • Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan
  • Yadda Sanusi II da Aminu Ado suka yi sallar Idi daban-daban a Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
  • Tsohon Alkalin Alkalan Najeriya, Lawal Uwais ya rasu
  • Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)