Aminiya:
2025-08-15@22:14:47 GMT

An kama wasu da haramtaccen buhunan takin zamani 20 a Borno

Published: 16th, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta kama wasu mutane uku da ake zargi ɗauke da buhuna 20 na haramtattun takin zamani samfurin “Urea”.

An bayyana hakan ne a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Borno DSP, Nahum Kenneth Daso ya fitar a ranar 15 ga Mayu, 2025.

Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka

Rundunar kai ɗaukin gaggawar (RRS), ƙarƙashin jagorancin Kwamishin ‘Yan sandan jihar CP Yusufu Mohammed Lawal ne ta kama waɗanda ake zargin a ranar 13 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 11:30 na safe a unguwar Tashan Journey, Maiduguri.

Waɗanda ake zargin sun haɗa da, Shamsuddeen Rabiu mai kimanin shekara 35, Malam Yau mai shekara 29, da Ibrahim Mohammed Sani mai shekara 30, suna jigilar takin zamanin da aka haramta samfurin urea ne, a cikin buhun taki na NPK a cikin keke NAPEP mai lamba GZA 17 ƁH Borno.

Rundunar ’yan sandan ta jaddada cewa, an haramta amfani da sinadarin urea a jihohi da dama ciki har da Jihar Borno, saboda yadda ‘yan ta’adda ke amfani da su wajen ƙera ababen fashewa.

Yanzu haka dai waɗanda ake zargin suna hannunsu, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike mai zurfi akan su.

Rundunar ’yan sandan jihar ta jaddada ƙudirinta na tabbatar da tsaro da tsaron al’ummar Jihar Borno, sannan ta buƙaci jama’a da su guji yin mu’amala da haramtattun abubuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan sandan Jihar Jihar Borno

এছাড়াও পড়ুন:

’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato

Dukkanin mutanen biyu na Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar, kuma za a gurfanar da su a kotu bayan an kammala bincike.

Kwamishinan ’Yansandan jihar, Emmanuel Olugbemiga Adesina, ya gargaɗi masu aikata laifi su daina ko su bar jihar.

Ya jaddada cewa rundunar za ta ci gaba da aiki don tabbatar da masu laifi sun fuskanci hukunci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu
  • Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 
  • An kama Mai Unguwa kan yi wa yarinya fyaɗe a Gombe
  • An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun
  • ’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato
  • An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati
  • ’Yan sanda sun kama matashi kan zargin aikata fashi a Gombe
  • Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe