Aminiya:
2025-07-01@07:44:40 GMT

An kama wasu da haramtaccen buhunan takin zamani 20 a Borno

Published: 16th, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta kama wasu mutane uku da ake zargi ɗauke da buhuna 20 na haramtattun takin zamani samfurin “Urea”.

An bayyana hakan ne a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Borno DSP, Nahum Kenneth Daso ya fitar a ranar 15 ga Mayu, 2025.

Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka

Rundunar kai ɗaukin gaggawar (RRS), ƙarƙashin jagorancin Kwamishin ‘Yan sandan jihar CP Yusufu Mohammed Lawal ne ta kama waɗanda ake zargin a ranar 13 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 11:30 na safe a unguwar Tashan Journey, Maiduguri.

Waɗanda ake zargin sun haɗa da, Shamsuddeen Rabiu mai kimanin shekara 35, Malam Yau mai shekara 29, da Ibrahim Mohammed Sani mai shekara 30, suna jigilar takin zamanin da aka haramta samfurin urea ne, a cikin buhun taki na NPK a cikin keke NAPEP mai lamba GZA 17 ƁH Borno.

Rundunar ’yan sandan ta jaddada cewa, an haramta amfani da sinadarin urea a jihohi da dama ciki har da Jihar Borno, saboda yadda ‘yan ta’adda ke amfani da su wajen ƙera ababen fashewa.

Yanzu haka dai waɗanda ake zargin suna hannunsu, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike mai zurfi akan su.

Rundunar ’yan sandan jihar ta jaddada ƙudirinta na tabbatar da tsaro da tsaron al’ummar Jihar Borno, sannan ta buƙaci jama’a da su guji yin mu’amala da haramtattun abubuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan sandan Jihar Jihar Borno

এছাড়াও পড়ুন:

  Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa

Kwamandan rundunar Kudus dake karkashin IRGC Birgediya janar Isma’ila Ka’a’ni ya bayyana cewa; Iran ta samu nasara, kuma nasara ce wacce za ta dore da yardar Allah.

Birgediya janar Isma’ila Ka’a’ni wanda ya halarci jana’izar shahidan ta’addancin HKI ya bayyana cewa; Daga yanzu zuwa gaba abinda yake gabanmu shi ne ci gaba da samun nasarori.

Haka nan kuma ya ce; Idan har aka samu hadin kai, aka yi aiki tare a tsakanin al’ummar kasa, to komai zai tafi daidai.”

Birgediya janar Ka’a’ni ya kuma jinjina wa shahidai, yana mai kara da cewa; tafarkinsu zai cigaba da wanzuwa.

A lokacin yakin kwanaki 12 HKI ta rika watsa  cewa ta kashe kwamandan na rundunar Kudus, lamarin da ya tabbata fargaganda ce.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
  • Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe
  • Iran: An Kama Wani Dan Leken Asirin “Mosad” A Tehran A Jiya Lahadi
  • Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
  •   Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa
  • An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Matsayin Kasarsa Na Rashin Mika Wuya Ga ‘Yan Kama Karya
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Jaddada Cewa: Iran Tana Da Hakkin Tace Sinadarin Uranium A Kasarta
  • Fararen hulan Isra’ila sun kai wa sojojin ƙasarsu hari
  • ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’