Aminiya:
2025-10-15@18:44:39 GMT

An kama wasu da haramtaccen buhunan takin zamani 20 a Borno

Published: 16th, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta kama wasu mutane uku da ake zargi ɗauke da buhuna 20 na haramtattun takin zamani samfurin “Urea”.

An bayyana hakan ne a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Borno DSP, Nahum Kenneth Daso ya fitar a ranar 15 ga Mayu, 2025.

Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka

Rundunar kai ɗaukin gaggawar (RRS), ƙarƙashin jagorancin Kwamishin ‘Yan sandan jihar CP Yusufu Mohammed Lawal ne ta kama waɗanda ake zargin a ranar 13 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 11:30 na safe a unguwar Tashan Journey, Maiduguri.

Waɗanda ake zargin sun haɗa da, Shamsuddeen Rabiu mai kimanin shekara 35, Malam Yau mai shekara 29, da Ibrahim Mohammed Sani mai shekara 30, suna jigilar takin zamanin da aka haramta samfurin urea ne, a cikin buhun taki na NPK a cikin keke NAPEP mai lamba GZA 17 ƁH Borno.

Rundunar ’yan sandan ta jaddada cewa, an haramta amfani da sinadarin urea a jihohi da dama ciki har da Jihar Borno, saboda yadda ‘yan ta’adda ke amfani da su wajen ƙera ababen fashewa.

Yanzu haka dai waɗanda ake zargin suna hannunsu, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike mai zurfi akan su.

Rundunar ’yan sandan jihar ta jaddada ƙudirinta na tabbatar da tsaro da tsaron al’ummar Jihar Borno, sannan ta buƙaci jama’a da su guji yin mu’amala da haramtattun abubuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan sandan Jihar Jihar Borno

এছাড়াও পড়ুন:

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

 

A nata bangare, Sima Bahous ta yabawa ci gaban da Sin ta samu wajen cike gibin fasahohi tsakanin jinsi, da ingiza ci gaban harkokin mata ta kowanne bangare da kare hakkoki da muradun mata.

 

Ta kuma yi kira ga kasa da kasa su hada hannu tare wajen karfafa gwiwar mata da ‘yan mata su samu ci gaba a zamanin amfani da fasahohi. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa  October 14, 2025 Daga Birnin Sin Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin October 14, 2025 Daga Birnin Sin Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya October 14, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
  • Ministan Yada Labarai Ya Bayyana Jihar Borno A Matsayin Mafi Juriya A Najeriya
  • Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali
  • Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
  • An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa
  • Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
  • Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa