A makon nan ne aka ga hotunan Sheikh Alƙali Zariya ya halarci zauren tattaunawa na fitacciyar jarumar Kannywood, Hadiza Aliyu Gabon, wanda ake kira ‘Gabon Talkshow’, abin da ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta.

Gabon Talkshow dandali ne da jaruma Hadiza ke gayyatar mashahuran jarumai da mawaƙa domin tattauna game da rayuwarsu da ayyukansu a masana’antar nishaɗi.

Tsaro: Tinubu ya ƙaddamar da rundunar tsaron daji a faɗin Najeriya Hauhawar farashi ya ragu zuwa kashi 23.71 — NBS

Bayyanar Sheikh Alƙali a wannan dandali ya jawo suka mai tarin yawa daga al’umma.

Wasu na ganin bai dace da matsayin malami irinsa ya halarci irin wannan dandali ba, domin ba wajen ilmantarwa ba ne ko karantarwa.

A cewar wasu, hakan zai iya rage darajar malamai a idon jama’a.

Sai dai kuma wasu na ganin babu laifi a yi hakan, tun da zauren tattaunawa ne da ake gayyatar mutane shahararru domin bayyana wasu ɓangarori na rayuwarsu da mutane ba su sani ba.

Wasu sun ce yin hakan na ƙara kusantar da malamai da jama’a ne.

Hakazalika, wasu sun ce ba Sheikh Alƙali ne malami na farko da ya halarci zauren Hadiza Gabon ba.

An ruwaito cewa a baya, jarumar ta taɓa gayyatar Sheikh Ibrahim Khalil, wanda shi ma ya halarta.

Sai dai duk da haka, akwai wasu daga cikin magoya bayan Sheikh Alƙali da suka bayyana rashin jin daɗinsu kan amsar goron gayyatar Hadiza Gabon.

Sun nuna damuwa da irin suka da zagi da ya biyo bayan halartar shirin da malaminsu ya yi.

Wani daga cikin magoya bayan Sheikh Alƙali, mai suna Ibrahim G. Lamara, ya wallafa a shafinsa na Facebook yana cewa: “Mu ‘yan Izala tsagin Jos, mu da su Yaseer Haruna Muhd, lallai ba ma jin daɗin zagin da Malam Alƙali Zariya yake janyo mana. Muna fata shugabanci zai yi maganin abin a wannan karo.”

Bayyanar Sheikh Alƙali a wannan zaure ya ƙara jaddada yadda malamai da mashahuran mutane ke fuskantar ɓangarori daban-daban daga al’umma, musamman a zamanin da kafafen sada zumunta ke da tasiri wajen bayyana ra’ayoyi cikin sauƙi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hira jaruma kannywood Sheikh Alƙali Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shi ma wasan da ta yi nasara a kan kungiyar Sifaniya a daf da za a tashi ta ci kwallon a gasar Zakarun Turai da na Newcastle United a Premier League. Tun daga nan alamomi suka fara bayyana cewar akwai tarin matsaloli a Liberpool, wadda kowanne wasa kwallo ke shiga ragarta in ban da wanda ta yi nasara a kan Arsenal 1-0 a Premier League cikin Agusta da wanda ta ci Burnley 1-0 a cikin watan Satumba a Premier League.

Sababbnin ‘Yanwasan da Liberpool ta saya a kakar banamages Giorgi Mamardashbili daga Balencia Jeremie Frimpong daga Bayern Leberkusen, Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen,

Milos Kerkez daga Bournemouth, Hugo Ekitike daga Eintracht Frankfurt, Aledander Isak daga Newcastle United, Armin Pecsi daga Puskas Akademia. Giobanni Leoni daga Parma Freddie Woodman daga Preston North, Will Wright daga Salford.

Wasu daga cikin matsalolin Liberpool A Yanzu

Matsalar masu buga mata tsakiya Liberpool ta samu sauye-sauye da yawa a fannin masu taka mata wasa daga tsakiya, bayan da wasu daga ciki suka bar kungiyar, ya dace a ce ta hada

fitattun da za ta fuskanci kakar bana.

Liberpool ta dauki Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen, amma har yanzu dan wasan bai nuna kansa ba, inda yake ta shan suka daga magoya bayan da suke ganin kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba.

Raunin ‘yanwasa da ke jinya

Raunin da wasu ‘yanwasan Liberpool suka ji sun taka rawar gani da kungiyar Liberpool ke kasa kokari a kakar nan. Daga ciki mai tsaron baya, Giobanni Leoni ya ji rauni a wasansa na farko a kungiyar, wanda ake cewa yana doguwar jinya. Mai tsaron raga Alisson Becker ya ji rauni a lokacin gasar zakarun turai wanda ake cewar zai yi jinya har karshen watan Oktoba, watakila ya wuce hakan.

Bayan Liberpool na yoyo

A kakar bara bayan Liberpool ya yi yoyo, duk da cewar kungiyar ce ta lashe kofin, amma dai an samu matsaloli da yawa a bayan. Kungiyoyi da dama sun amfana da kurakuren Liberpool a bara daga ciki har da Nottingham Forest da Brighton da kuma Brentford.

Wasu lokutan da zarar Liberpool ta kai kora sai kaga wagegen gibi tsakanin masu tsare baya da ‘yan tsakiya. Haka kuma tun kafin fara kakar bana, Liberpool ta buga wasannin atisaye, kuma tun a lokacin gurbin masu tsare baya ya nuna matasalar da kungiyar za ta iya fuskanta da fara

kakar nan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025 Wasanni Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray October 30, 2025 Wasanni Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi October 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Ko Kawo Dakarun Kasar Amurka Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda