Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa 50 A Yankin Zirin Gaza
Published: 6th, May 2025 GMT
Falasdinawa fiye da 50 ne suka yi shahada yayin da wani adadi da dama suka jikkata a hare-haren da sojojin mamayar Isra’ila suka kai Gaza a jiya Litinin
Rahotonni sun bayyana cewa: Fiye da Falasdinawa 50 ne aka suka yi shahada wasu adadi da dama kuma suka jikkata sakamakon hare-haren da sojojin mamayar Isra’ila ke ci gaba da kai kan yankin Zirin Gaza na Falasdinu.
A wani labarin kuma, Falasdinawa a yankin Al-Karama da ke arewacin zirin Gaza sun farka da wani sabon kisan kiyashi da jiragen saman yakin haramtacciyar kasar Isra’ila suka yi bayan da suka kai hari kan wani ginin fararen hula, lamarin da ya yi sanadiyar shahadan Falasdinawa da dama da kuma jikkata.
A tsakiyar daren jiya ne jiragen yakin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kai hare-hare kan wani gini mai hawa uku, inda suka yi sanadiyyar shahada Falasdinawa kusan 20, kuma har yanzu ba a gano wasu gawarwakin ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Isra ila suka
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinu : ‘Yan jarida 222 aka kashe tun fara yakin Gaza
Bayanai daga falasdinu na cewa an kashe ‘yan jarida 5 na Falasdinawa a wasu hare-hare daban-daban da Isra’ila ta kai a zirin Gaza, lamarin da ya kai adadin ma’aikatan yada labaran da aka kashe tun farkon yakin Isra’ila a zirin Gaza zuwa 222.
Daga cikin wadanda harin ya rutsa da su har da dan jarida mai daukar hoto Aziz al-Hajjar, da matarsa, da ‘ya’yansu, wadanda aka kashe a ranar Lahadi, lokacin da jiragen yakin Isra’ila suka kai hari a gidansu da ke unguwar Saftawi a arewacin Gaza.
A gefe guda kuma, an kashe dan jarida Ahmad al-Zinati tare da matarsa, Nour al-Madhoun, da ‘ya’yansu, Mohammad da Khaled, a lokacin da aka kai wa tantin su hari a Khan Younis a yammacin ranar Asabar.
Shahadar wadannan ‘yan jarida na zuwa ne kwanaki biyu kacal bayan mutuwar Ahmed al-Halou, wani dan jarida da ke aiki da kafar yada labaran birnin Quds, wanda aka kashe a wani harin da Isra’ila ta kai a zirin Gaza.