Falasdinawa fiye da 50 ne suka yi shahada yayin da wani adadi da dama suka jikkata a hare-haren da sojojin mamayar Isra’ila suka kai Gaza a jiya Litinin

Rahotonni sun bayyana cewa: Fiye da Falasdinawa 50 ne aka suka yi shahada wasu adadi da dama kuma suka jikkata sakamakon hare-haren da sojojin mamayar Isra’ila ke ci gaba da kai kan yankin Zirin Gaza na Falasdinu.

Daga cikin hare-haren har da hare-haren da jiragen mamayar Isra’ila suka kai kan wani gini mai yawan jama’a a unguwar Al-Karama da ke arewacin Gaza, wanda ya yi sanadin kisan kiyashi kan mutane ciki har da mata da kananan yara 20 da kuma fararen hula na daban.

A wani labarin kuma, Falasdinawa a yankin Al-Karama da ke arewacin zirin Gaza sun farka da wani sabon kisan kiyashi da jiragen saman yakin haramtacciyar kasar Isra’ila suka yi bayan da suka kai hari kan wani ginin fararen hula, lamarin da ya yi sanadiyar shahadan Falasdinawa da dama da kuma jikkata.

A tsakiyar daren jiya ne jiragen yakin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kai hare-hare kan wani gini mai hawa uku, inda suka yi sanadiyyar shahada Falasdinawa kusan 20, kuma har yanzu ba a gano wasu gawarwakin ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila suka

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta sanar da cewa: Ta gabatar da martani mai kyau ga shawarar dakatar da bude wuta tsakaninta da gwamnatin mamayar Isra’ila

Kungiyar Hamas ta sanar da kammala tuntubarta tare da gabatar da kyakkyawar amsa ga sabuwar shawarar neman dakatar da bude wuta, inda ta bayyana shirinta na nan take na yin shawarwari kan tsarin aiwatarwa.

Kungiyar gwagwarmayar Musulunci a Falastinu ta Hamas ta sanar a yammacin jiya Juma’a cewa ta kammala shawarwarin cikin gida da kuma tuntubar wasu bangarori da dakarun Falasdinawa dangane da sabuwar shawara da masu shiga tsakani suka gabatar na dakatar da hare-haren wuce gona da iri kan al’ummar Falasdinu a zirin Gaza.

Kungiyar ta yi nuni da cewa ta mika martanin ta ga ‘yan uwanta da ke shiga tsakani, inda ta tabbatar da cewa martanin yana da kyau. Ta sake nanata cewa a shirye take ta gaggauta shiga wani zagaye na tattaunawa kan hanyoyin aiwatar da wannan tsarin.

A cikin wannan mahallin, kafofin watsa labaru na haramtacciyar kasar Isra’ila sun ba da rahoton cewa, an sami wasu muhimman sauye-sauye a daftarin na Witkoff, wanda dukkansu ke goyon bayan Hamas.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila
  • Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  •   Gaza: Fiye Da Falasdinawa 17 Ne Su Ka Yi Shahada Ayau Juma’a
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa
  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
  • Falasdinawa Kimani 40,000 HKI Ta Kora Daga Yankin Yamma Da Kogin Jordan
  • Ben Gafir Ya Bukaci Gwamnatin HKI Ta Mamaye Yankin Gaza Gaba daya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata