Iran Ta Mayar Da Martani Akan Zarginta Dangane Da Yemen
Published: 5th, May 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta yi watsi da zarge-zargen da aka yi ma ta dangane da kasar Yemen.
A wani bayani da ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran din ta fitar ta bayyana cewa: Abinda mutanen Yemen suke yi domin taimakawa al’ummar Falasdinu, mataki ne na kashin kansu da su ka dauka cikin ‘yanci saboda lamirinsu na ‘yan adamtaka da kuma taimako na musulunci ga ‘yan’uwansu Falasdinawa.
Bayanin ya kuma ci gaba da cewa; Jinginawa jamhuriyar musulunci ta Iran abinda mutanen na Yemen suke yi, ba shi da tushe, kuma manufar hakan ita ce, rufe laifukan da ‘yan sahayoniya suke yi a Falasdinu.”
Bayanin ya kuma ce; Jamhuriyar musulunci tana sake jaddada matsayarta akan wajabcin kiyaye da karrama kasashe da kasantuwarsu a dunkule a wuri daya, kamar kuma yadda muke yin tir da hare-haren sojan Amurka akan Yemen, domin hakan take dokokin MDD ne, da kuma dokokin kasa da kasa.”
Haka nan kuma ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta yi kira da a kawo karshen kisan kiyashin da ‘yan sahayoniya suke yi wa Falasdinawa da shi ne tuhsen rashin zaman lafiya a cikin wannan yankin na yammacin Asiya.
Wani sashe na bayanin na ma’aikatar harkokin wajen jamhuriyar musulunci ta Iran din ya ce; al’ummar Iran a shirye suke, su kare kansu daga duk wata barazana akan manufofin kasa, kuma alhakin duk abinda zai faru yana wuyan hukumomin ‘yan ta’adda na Amurka da sahayoniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: ma aikatar harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
Sanarwar ta ƙara da cewa ana aiki tare da hukumomin cikin gida da na ƙasa da ƙasa domin ganin an gudanar da aikin kwasar cikin tsaro.
Sanarwar ta ce: “Ma’aikatar Harkokin Waje na sanar da jama’a cewa, sakamakon rikicin da ke ƙara ƙamari tsakanin Isra’ila da Iran, Gwamnatin Tarayya tana shirin ƙarshe na kwaso ‘yan Nijeriya da suka maƙale a waɗannan ƙasashe.
“Saboda haka, ana shawartar dukkanin ‘yan Nijeriya da abin ya shafa da su kiyaye matakan tsaro da kuma tuntuɓar ofishin jakadanci mafi kusa domin yin rijista da samun ƙarin umarni.”
Baya ga haka, Gwamnatin Tarayya ta sake kira da a dakatar da faɗa tsakanin Isra’ila da Iran, tare da buƙatar ɓangarorin su rungumi tattaunawa, su mutunta dokokin kare haƙƙin ɗan Adam na duniya, kuma su bai wa rayuwar fararen hula muhimmanci.
Ma’aikatar ta jaddada cewa Nijeriya na goyon bayan hanyoyin warware rikici ta hanyar lumana da kuma tallafa wa zaman lafiya a yankuna da duniya baki ɗaya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp