Hamas Ta Yaba Da Ma’aikaciyar Kamfanin Microsoft Wacce Ta Fallasa Yadda Kamfanin Yake Taimakawa HKI

Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza, ta yabawa ma’aikaciyar kamfanin kayakin lantarki da kuma sadawar ta Microsof mai suna Ibtihal Abussad wacce ta fallasa kamfanin a bikin cika shekaru 50 da kafa shi, a dai dai lokacinda daractan kamfanin mai kula da sashen AI kirkirerren fasaha Mustafa Sulaiman yake jawabi.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta kara da cewa Abussad ta tilastawa daraktan yanke maganarsa, inda ta fara cewa abun kunya ne kamfanin Microsuft yana taimakawa HKI da fasahar Ai ko kirkirerren fasaha a kissan kiyashin da take yi a gaza. Ta kuma fallasa yadda manya manyan kamfanonin sadanarwan da kuma kayakin lantarki suke da hannu dumu-dumu a kisan kiyashin da ke faruwa a Gaza.

Daga karshen kungiyar Hamas ta bukaci sauran masana irin Ibtihal su koyi jarunta wajenta su kuma fallasa wadanda suka tabbatar da suna da hannu a yakin gaza.

Ya zuwa yanzu dai HKI ta kashe falasdinawa kimani 50,700 tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda aka dawo da ’yan Najeriya 203 daga Libya

Kalli yadda aka karɓi ’yan Najeriya guda 203 da aka dawo da su daga ƙasar Libya.

(Hoto: Onyekachukwu Obi).

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • HOTUNA: Yadda aka dawo da ’yan Najeriya 203 daga Libya
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara