’Yan acaba sun yi wa mai fura fyaɗe Abuja
Published: 2nd, May 2025 GMT
Jami’an tsaron sa kai sun kama wasu abokai biyu masu sana’ar acaba, bisa zargin yin fyaɗe ga wata Bafulatana mai tallar fura da nono a Yankin Babban Birnin Tarayya Abuja.
Wani jami’in tsaron sa kai, Usman Dantala, ya ce abokan biyu sun yi wa Bafulatanar fyade ne da tsakar rana a yankin Ikwa da ke Ƙaramar Hukumar Gwagwalada.
Ya bayyana cewa ranar Asabar da misalin karfe 2:12 na rana ne abokan biyu suka yaudari mai faurar ’yar kimanin shekaru 19 zuwa daƙin wani abokinsu inda suka yi mata fyade.
Jami’in ya ce, sun kira Bafulatanar ne da cewa za ta sayar musu da nono a gidan wani abokinsu. A can ne suka yaudare ta shiga daƙin suka kuma yi mata fyade.
An kama matashi kan ‘satar’ ’yar maƙwabcinsa Wulaƙancin da ake mana a Kudu ya yi yawa —Hausawan LegasDantala ya ce wani maƙwabci ne ya ji hayaniya daga daƙin ta tagarsa, wanda hakan ya sa fita ya sanar da jama’a.
“Nan take makwabcin ya sanar da sauran mutane, waɗanda suka ruga zuwa daƙin, inda suka samu mai furar tana kuka a tuɓe, yayin da ɗaya daga cikin samarin ya tsere.”
Ya ce jami’an sun kama ɗayan wanda ake zargin, wanda kuma ya kai su wata daba inda suka kama ɗayan ma.
Daga baya jami’an sun kai mai furar asibiti, inda aka tabbatar da cewa an yi lalata da ita; aka miƙa waɗanda ake zargin ga ’yan sanda.
Kakakin ’yan sanda ta Abuja, SP Josephine Adeh, ba ta samu damar yin tsokaci kan wannan lamari ba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250 a Jami’ar Ilorin
Babban attajirin Afirka kuma Shugaban Rukunin Kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya ɗauki nauyin gina ɗakunan kwanan ɗalibai masu gadaje 250 da Babban Masallacin Juma’a na Ilorin ya tsara a Jami’ar Ilorin da ke Jihar Kwara.
An kiyasta aikin zai ci kusan naira biliyan 1.1, kuma an ƙaddamar da shi ne domin samar da hanyar samun kuɗin kula da masallacin.
Ana sa ran kuɗaɗen haya da za a samu daga ɗaliban da za su zauna a wurin zai rika shiga asusun kula da masallacin.
Sakataren kwamitin amintattu na masallacin, Alhaji Shehu AbdulGafar, ya shaida wa manema labarai a Ilorin cewa Ɗangote ya riga ya sanar da su cewa zai ɗauki nauyin aikin gaba ɗaya.
Cire tallafin man fetur shi ne abin da ya dace —Sarki Sanusi II NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar RuwaYa ce an riga an rattaba hannu kan yarjejeniya da Jami’ar Ilorin wadda ta ba wa masallacin damar mallaka da gudanar da ɗakin kwanan ɗaliban na tsawon shekaru 21 kafin a miƙa shi ga jami’ar.
Baya ga aikin ginin, Ɗangote ya kuma yi alƙawarin bayar da tallafin Naira miliyan 5 a kowane wata domin kula da masallacin har sai an kammala aikin.
AbdulGafar ya ce wannan taimako zai rage nauyin kuɗin aikin, tare da tabbatar da ɗorewar ayyukan masallacin.
Ya ƙara da cewa ɗakin kwanan zai taimaka wajen rage matsalar ƙarancin wurin kwana ga ɗaliban jami’ar.
Shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki sun yaba wa Ɗangote, sun bayyana wannan mataki a matsayin abin koyi na yadda za a iya haɗa kai tsakanin cibiyoyin addini da ’yan kasuwa wajen ci-gaban al’umma.