HausaTv:
2025-11-03@06:23:50 GMT

Iran ta ce an dage tattaunawar matakin kwararru da Amurka zuwa ranar Asabar

Published: 23rd, April 2025 GMT

Iran ta sanar da dage tattaunawar da aka shirya gudanarwa yau Laraba tsakanin tawagar kwararu ta kasar da kuma na Amurka a kasar Oman a wani bangare na ci gaba da tattaunawar da ake tsakanin kasashen biyu kan shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ya bayyana cewa, an dage tattaunawar ta matakin kwararru tsakanin Iran da Amurka kan cikakkun bayanai na fasaha na yiwuwar maye gurbin yarjejeniyar nukiliyar shekarar 2015, wadda aka shirya yi a yau ranar Laraba, zuwa ranar mai zuwa 26 ga watan Afrilu.

Esmaeil Baghaei ya bayyana cewa, za a gudanar da taron a daidai lokacin zagaye na gaba na tattaunawar tsakanin jagororin tawagogin guda biyu.

Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi da Steve Witkoff, manzon musamman na shugaban Amurka kan harkokin yankin gabas ta tsakiya, sun jagoranci tattaunawar wacce ba ta kai tsaye ba har sau  biyu kan shirin nukiliyar Iran da kuma dage takunkumin da Amurka ta kakaba wa Iran a babban birnin Oman na Muscat da babban birnin Italiya, Roma, a ranakun 12 da 19 ga watan Afrilun nan, a shiga tsakanin Ministan harkokin wajen Omani Badr bin Hamad Al Busaidi ne ya shiga tsakani tattaunawar.

A ranar 26 ga watan Afrilu ne ake sa ran gudanar da zagaye na uku na shawarwarin kai tsaye tsakanin Araghchi da Witkoff a kasar Oman domin tantance sakamakon tarukan da masana suka yi da kuma auna yadda suke kusa da cimma matsaya.

A wani labara kuma, ministan harkokin wajen Iran, Araghchi ya tattauna da shugaban hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya, ta IAEA, jiya Talata

Inda ya yi masa bayani kan sabbin abubuwan da suka faru game da tattaunawar da Amurka, yana mai jaddada kudurin Iran na yin shawarwarin bil hakki.

Shi ma Grossi, ya yaba da matakin da Iran ta dauka, ya kuma bayyana shirin hukumar na bayar da duk wani taimako a cikin wannan tsari, daidai da ayyukanta da ikonta kamar yadda dokar hukumar ta IAEA ta ayyana.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya

Ministan harkokin wajen kasar iran Abbas Araqchi a wata hira da yayi da gidan talabijin din Aljazeera ya gargadi isra’ila kuma yayi cikakkan bayani kan shirin nukiliyar iran na zaman lafiya , da kuma halin da yankin ke ciki da yi yuwar sake komawa teburin  tattaunawa da kasar Amurka.

Wannan bayani yazo ne adaidai lokacin da lamura ke kara zafi a yankin  bayan yakin da aka yi tsakanin iran da kuma Israila,  don haka bayanan na Araqchi wata sanarwa ce dake nuna shirin iran na mayar da martani amma kuma tabar kofar tattaunawar diplomasiya  a bude.

Har ila yau ministan ya bayyana cewa iran a shirye take ta tunkari duk wani kalu-bale, kuma za ta mayar da martani mai karfi game da duk wani wuce gona da irin Isra’ila, don mun shirye fiye da kowanne lokaci a baya, kuma yayi gargadin cewa isra’ila za ta sake shan wani kayen idan ta kara shelanta yaki akan iran a nan gaba,

Yace isra’ila tana kokarin kara fadada rikicin yanki ne ta hanyar kai hari kan abubuwan manfetur din kasar iran, yace isra’ila ba za ta iya shiga wani yaki ba ba tare da samu amincewar Amurka ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania November 1, 2025  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare