HausaTv:
2025-06-15@10:09:29 GMT

Iran ta ce an dage tattaunawar matakin kwararru da Amurka zuwa ranar Asabar

Published: 23rd, April 2025 GMT

Iran ta sanar da dage tattaunawar da aka shirya gudanarwa yau Laraba tsakanin tawagar kwararu ta kasar da kuma na Amurka a kasar Oman a wani bangare na ci gaba da tattaunawar da ake tsakanin kasashen biyu kan shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ya bayyana cewa, an dage tattaunawar ta matakin kwararru tsakanin Iran da Amurka kan cikakkun bayanai na fasaha na yiwuwar maye gurbin yarjejeniyar nukiliyar shekarar 2015, wadda aka shirya yi a yau ranar Laraba, zuwa ranar mai zuwa 26 ga watan Afrilu.

Esmaeil Baghaei ya bayyana cewa, za a gudanar da taron a daidai lokacin zagaye na gaba na tattaunawar tsakanin jagororin tawagogin guda biyu.

Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi da Steve Witkoff, manzon musamman na shugaban Amurka kan harkokin yankin gabas ta tsakiya, sun jagoranci tattaunawar wacce ba ta kai tsaye ba har sau  biyu kan shirin nukiliyar Iran da kuma dage takunkumin da Amurka ta kakaba wa Iran a babban birnin Oman na Muscat da babban birnin Italiya, Roma, a ranakun 12 da 19 ga watan Afrilun nan, a shiga tsakanin Ministan harkokin wajen Omani Badr bin Hamad Al Busaidi ne ya shiga tsakani tattaunawar.

A ranar 26 ga watan Afrilu ne ake sa ran gudanar da zagaye na uku na shawarwarin kai tsaye tsakanin Araghchi da Witkoff a kasar Oman domin tantance sakamakon tarukan da masana suka yi da kuma auna yadda suke kusa da cimma matsaya.

A wani labara kuma, ministan harkokin wajen Iran, Araghchi ya tattauna da shugaban hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya, ta IAEA, jiya Talata

Inda ya yi masa bayani kan sabbin abubuwan da suka faru game da tattaunawar da Amurka, yana mai jaddada kudurin Iran na yin shawarwarin bil hakki.

Shi ma Grossi, ya yaba da matakin da Iran ta dauka, ya kuma bayyana shirin hukumar na bayar da duk wani taimako a cikin wannan tsari, daidai da ayyukanta da ikonta kamar yadda dokar hukumar ta IAEA ta ayyana.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka

Da yake nasa jawabin, Sangare ya ce, Nijar na bin manufar Sin daya tak a duniya, kuma tana ba da fifiko ga hadin gwiwarta da kasar Sin, da mayar da hankali sosai kan harkokin tsaro, kana tana son kara amincewa da juna, da ci gaba da yin shawarwari bisa mutunta juna a tsakaninsu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya