Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan ya bayyana cewa JMI ba zata taba jada baya a kan shirinta na makamashin Nukliya ba, kuma yayi allawadai da duka wani shiri na kaiwa cibiyoyin nukliyar kasar Hare-hare.

Tashar talabijin ta Presstv ta nakalto shugaban yana fadar haka a taron raya ranar Nukliya ta karo karo na 19 a wanda aka gudanar a nan Tehran.

Shugaban ya kara da cewa, Iran bata neman yaki da kowa, amma zata maida martani kan duk wata takala daga HKI ko Amurka. Ya ce Iran ba zata amince wani ya hana mutanen kasar amfani da fasahar da All..ya hore masu ba. Ya kuma kara jaddada cewa JMI bata neman mallakar makaman Nukliya.

A rana irin ta yau ce wato 9 ga watan Afrilun shekara ta 2006, masana fasahar nukliya na JMI suka sami nasara a karon farko suka samar da makamashi daga fasahar nukliya tare da amfani da sinadarin Uranium.

A yau shekaru 19 kenan tun lokacin kasar take samun ci gaba a fasahar Nukliya da kuma amfaninsa. Inda ya ma kasar ta kaddamarda sabbin ci gaban da ta samu tare da amfani da makamacin Nukliya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan

Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi ya gana da Shugaban Eritrea Isaias Afwerki domin tattauna halin da ake ciki a yankin,  Shugaba al-Sisi ya tabbatar da jajircewar Masar wajen tallafawa ‘yancin kai da kuma ‘yancin yankin Eritrea.

A yayin taron, wanda Ministan Harkokin Wajen Masar Badr Abdel-Aty da takwaransa na Eritrea, Osman Saleh Mohammed suka halarta, shugabannin biyu sun tattauna halin da ake ciki a yankin.

Sun tabbatar da hangen nesansu kan hanyoyin kawo karshen yakin a Sudan, suna masu  jaddada bukatar tallafawa cibiyoyin gwamnati na kasa, musamman Sojojin Sudan, tare da kin amincewa da duk wani yunkuri na kafa hukumomi ko cibiyoyi  masu kishiyantar gwamnati a kasar.

Shugaba al-Sisi ya jaddada matsayar Masar da kuma  kokarin da take yi  don kawo karshen yakin da kuma rage wahalhalun jin kai na al’ummar Sudan, ta hanyar yin aiki tare da abokan huldar Masar  don tabbatar da hadin kan Sudan, mutuncin yankin, da kuma ‘yancin kan kasa.

A nasa bangaren, Shugaba Afwerki ya nuna matukar godiyarsa ga rawar da y ace Masar tana  takawa karkashin jagorancin Shugaba El-Sisi, wajen karfafa zaman lafiya da kuma kokarin ci gaban  yankin kusurwar Afirka da Gabashin Afirka. Ya yi maraba da fadada hadin gwiwar tattalin arziki da Masar da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu kan batutuwan kasa da kasa da na yanki masu amfani ga junansu.

Taron ya kuma yi magana kan sabbin abubuwan da suka faru a Somaliya, inda Shugabannin biyu sun jaddada kudurin kasashensu na amincewa da sanarwar hadin gwiwa da aka fitar a taron kolin Masar, Eritrea, da Somaliya a Asmara a watan Oktoban 2014, wanda ya tabbatar da wajibcin girmama ka’idoji da dokokin kasa da kasa, musamman ma cikakken yankin Somaliya da dukkan kasashen yankin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai
  • Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa