Aminiya:
2025-04-30@18:57:46 GMT

Fulham ta doke Liverpool bayan wasa 26 a jere ba tare da rashin nasara ba

Published: 7th, April 2025 GMT

Fulham ta kawo ƙarshen wasanni 26 da Liverpool ta yi a jere ba tare da rashin nasara ba a gasar Firimiyar Ingila ta wannan kakar.

Fulham ta yi nasarar doke Liverpool da 3-2 a Craven Cottage ranar Lahadi a wasan mako na 31.

Liverpool ce ta fara zura ƙwallo a ragar Fulham ta hannun Mac Allister minti 14 da fara wasa kafin Ryan Sessegnon ya rama wa Fulham a minti 23.

Fulham ba ta yi ƙasa a gwiwa ba sai da ta ƙara wa Liverpool ƙwallo ɗaya a lokacin da ɗan wasan Nijeriya, Alex Iwobi ya zura ƙwallo a ragar Liverpool a minti 32 da fara wasa.

Yayin da ake tunanin cewa Liverpool za ta iya ramawa, sai Fullham ta ƙara mata ƙwallo na uku a lokacin da Rodrigo Muniz ya zura ƙwallo a ragar Liverpool minti 37 da fara wasa.

An dai tafi hutun rabin lokaci Fullham na da rinjaye a kan Liverpool da ci 3-1 yayin da ake tunanin cewa komai na iya faruwa idan aka dawo daga hutun.

Bayan an dawo daga hutun rabin lokaci, Liverpool ta yi ta ƙoƙarin ɗaukar fansa domin ta samu ko da maki ɗaya ne daga wasan, sai dai haƙarta bai cim ma ruwa ba har sai minti 72 da fara wasa.

A minti 72 da fara wasan ne Luiz Diaz ya zura ƙwallo ɗaya a ragar Fullham lamarin da ya mayar da wasan 3-2.

Sai dai kuma Liverpool ba ta iya ƙara wa Fulham ba domin Fulham ta samu ta kare rinjayenta a wasan kuma ta cinye maki ukun wasan gaba ɗaya.

Duk da wannan sakamako, Liverpool ce ke ci gaba da jan ragama a saman teburin gasar Firimiya da maki 73 duk da cewa ba ta ƙara ratar da ta bai wa Arsenal da ke biye da ita ba.

Ita kuwa Fulham tana ta takwas a teburin gasar Firimiya inda take da maki 48.

Kociyan Liverpool, Arne Slot wanda ya ce kungiyarsa ta cancanci wannan sakamako, ya tabbatar da cewa ’yan wasansa sun tafka kura-kurai da ya zama tilas su dauki izina a kai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arne Slot Firimiyar Ingila da fara wasa zura ƙwallo

এছাড়াও পড়ুন:

Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Muhammad Sa’ad, ya bayyana cewa gobe Talata, 30 ga watan Afrilun 2025, ita ce za ta kasance 1 ga watan Zhul Qi’ida na shekarar 1446 ta Hijiriyya.

Wata sanarwa da shugaban kwamatin ganin wata na fadar, Farfesa Sambo Wali ya fitar ta ce an ɗauki matakin ne saboda ba a ga jinjirin watan ba a ranar Lahadi.

Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine

Hakan na nufin yau Litinin, 28 ga watan Afrilu ne 30 ga watan Ƙaramar Sallah na Shawwal.

A ƙa’idar kalandar Musulunci, kowane wata yana yin kwana 29 ne, amma idan ba a ga jaririn watan ba sai a cika shi zuwa kwana 30.

Aminiya ta ruwaito cewa tun a ranar Asabar da ta gabata ce Fadar Sarkin Musulmin ta ba da umarnin duban watan na Zhul Qi’ida.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi
  • Liverpool Sun Zama Zakaran Gasar Premier Bayan Lallasa Tottenham