Aminiya:
2025-07-31@16:52:03 GMT

Fulham ta doke Liverpool bayan wasa 26 a jere ba tare da rashin nasara ba

Published: 7th, April 2025 GMT

Fulham ta kawo ƙarshen wasanni 26 da Liverpool ta yi a jere ba tare da rashin nasara ba a gasar Firimiyar Ingila ta wannan kakar.

Fulham ta yi nasarar doke Liverpool da 3-2 a Craven Cottage ranar Lahadi a wasan mako na 31.

Liverpool ce ta fara zura ƙwallo a ragar Fulham ta hannun Mac Allister minti 14 da fara wasa kafin Ryan Sessegnon ya rama wa Fulham a minti 23.

Fulham ba ta yi ƙasa a gwiwa ba sai da ta ƙara wa Liverpool ƙwallo ɗaya a lokacin da ɗan wasan Nijeriya, Alex Iwobi ya zura ƙwallo a ragar Liverpool a minti 32 da fara wasa.

Yayin da ake tunanin cewa Liverpool za ta iya ramawa, sai Fullham ta ƙara mata ƙwallo na uku a lokacin da Rodrigo Muniz ya zura ƙwallo a ragar Liverpool minti 37 da fara wasa.

An dai tafi hutun rabin lokaci Fullham na da rinjaye a kan Liverpool da ci 3-1 yayin da ake tunanin cewa komai na iya faruwa idan aka dawo daga hutun.

Bayan an dawo daga hutun rabin lokaci, Liverpool ta yi ta ƙoƙarin ɗaukar fansa domin ta samu ko da maki ɗaya ne daga wasan, sai dai haƙarta bai cim ma ruwa ba har sai minti 72 da fara wasa.

A minti 72 da fara wasan ne Luiz Diaz ya zura ƙwallo ɗaya a ragar Fullham lamarin da ya mayar da wasan 3-2.

Sai dai kuma Liverpool ba ta iya ƙara wa Fulham ba domin Fulham ta samu ta kare rinjayenta a wasan kuma ta cinye maki ukun wasan gaba ɗaya.

Duk da wannan sakamako, Liverpool ce ke ci gaba da jan ragama a saman teburin gasar Firimiya da maki 73 duk da cewa ba ta ƙara ratar da ta bai wa Arsenal da ke biye da ita ba.

Ita kuwa Fulham tana ta takwas a teburin gasar Firimiya inda take da maki 48.

Kociyan Liverpool, Arne Slot wanda ya ce kungiyarsa ta cancanci wannan sakamako, ya tabbatar da cewa ’yan wasansa sun tafka kura-kurai da ya zama tilas su dauki izina a kai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arne Slot Firimiyar Ingila da fara wasa zura ƙwallo

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya

Fadar Shugaban ƙasa ta bayyana cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙarin wa’adin shekara guda ga shugaban hukumar Kwastan ta Nijeriya, Bashir Adewale Adeniyi.

Kafin wannan ƙarin wa’adin, aikin Adeniyi zai kare ne a ranar 31 ga Agusta, 2025. Sai dai sanarwar da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis ta ce wannan mataki na Tinubu zai ba Adeniyi damar kammala muhimman gyare-gyare da ayyuka da gwamnatin ke aiwatarwa a hukumar.

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

A cikin manyan ayyukan da ake son a kammala akwai shigar da cigaban zamani da ake yi wa hukumar Kwastan, da aiwatar da tsarin “National Single Window Project” da kuma cika alƙawuran Nijeriya a ƙarƙashin yarjejeniyar cinikayyar Afrika (AfCFTA).

“Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya” in ji sanarwar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
  • Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
  • Man Utd Na Tattaunawa Da Golan PSG, Chelsea Ta Nace Wa Garnacho
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza