Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i
Published: 21st, March 2025 GMT
Sun kuma bayyana cewa, wajibi ne gwamnati ta mayar da hankali wajen inganta manyan makarantun da ake da su na tarayya da kuma jihohi, ta hanyar samar da wadatattun kudade, inganta abubuwan more rayuwa da kuma tabbatar da ganin ma’aikatan jami’i’on, sun samu horo na musamman da suke bukata da kuma tallafa musu.
Wani mai ba da shawara a kan harkokin binciken ilimi a Jami’ar Abuja, Humphrey Ukeaja, ya gano wasu damammaki da kalubale iri-iri da aka samu kwanan nan.
Masanin ya yi nuni da cewa, rashin samun wadatattun kudade a fannin ilimi a Nijeriya, ya zama wani babban al’amari. “Idan kuna son yin wannan sauyi misali, mayar da jami’i’o’i zuwa na gwamnatin tarayya, har yanzu a kwai ayar tambaya, shin za ku inganta su ne kokuwa inganta kudaden da za a bai wa sabbin jami’o’in? Domin kuwa, wannan ba karamin kalubale ba ne. saboda haka, gwamnati tana da kyakkyawan kudiri ne na daukar cikakken nauyin wannan ilimi?”.
Canzawa tare da kara wasu makarantu ba tare da daukar cikakken nauyinsu ba, zai sa ba za su iya tsayawa da kafafunsa, wanda a karshe ko kadan ba za a samu abin da ake nema ba na biyan bukata, in ji shi.
Farfesa Ukeaja, na da ra’ayin cewa, kafa jami’o’in tarayya a wurare kamar Kachia, zai taimaka wajen inganta ilimi tare da rage tazarar da ke tsakanin birane da kauyuka ta fannin samar da ilimi. “Don haka, idan har za a samar da jami’o’i a wuraren da suka dace, babu shakka wannan zai zama wani babban ci gaba”, in ji shi.
Ya ba da shawarar cewa, ya kamata gwamnatin tarayya ta kara yawan kudade ga fannin ilimi tare da fadada hadin gwiwa da jami’o’i masu zaman kansu, domin inganta jami’o’in, bai wa malamai horo na musamman da sauran makamantansu.
Har ila yau, kungiyar daliban Nijeriya; sun yaba da matakin, amma kuma sun nuna damuwa a kan lamarin.
Jami’in hulda da jama’a na kungiyar dalibai ta kasa (NANS), Kwamared Samson Ajasa Adeyemi, ya bayyana jin dadinsa kan kokarin da gwamnatin tarayya ke yi na magance matsalolin ilimi a Nijeriya, musamman kan yadda take mayar da makarantun jihohi zuwa na tarayya.
Sai dai ya koka da cewa, daya daga cikin manyan kalubalen da ke fuskantar fannin na ilimi a Nijeriya, ya hada da rashin isasssun kudade.
Ajasa ya yi nuni da cewa, da dama daga cikin wadannan manyan makarantun gwamnati, sun dogara ne da kudaden basussuka wajen tafiyar da makarantun, sannan akwai bukatar aiwatar da gaskiya wajen aiwatar da kasafin kudin yadda ya kamata, domin tabbatar da ganin an yi amfani da wadannan kudade yadda ya dace.
A nasa bangaren, wani dan kishin kasa, Mista Tochukwu Osuagwu, ya bukaci gwamnati ta kara zuba hannun jari a jami’o’in da ake da su, domin inganta su yadda ya kamata.
“Me zai hana a mayar da hankali wajen inganta jami’o’in da ake da su a fadin wannan kasa baki-daya, ko shakka babu, Nijeriya za ta ci gaba idan muka riki junanmu da gaskiya.
“A bayyane yake cewa, jami’o’inmu na cikin wani mummunan yanayi, wanda ba haka ya kamata al’amarin ya kasance ba, kyautuwa ya yi a ce jami’o’inmu sun samu wadatattun kayan aiki da ci gaba kamar yadda ake gani a wasu sauran kasashe”, in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
A wani gagarumin ci gaba na inganta walwala da ci gaban yara da matasa wadanda suka isa makaranta, Shugaban Hukumar Kula da Ilimin Farko ta Jihar Nasarawa NSUBEB, Dokta Kasim Mohammed Kasim ya karbi tawagar Kids & Teens Resource Center K&TRC a wani taron bayar da shawarwari da aka mayar da hankali kan shirin Ilimi don Lafiya da walwala, wanda UNESCO ke tallafawa.
An gudanar da babban taron ne a hedkwatar Hukumar NSUBEB, inda ya samu halartar kwamishinonin hukumar su uku, da Daraktoci da dama, da kuma tawagar K&TRC karkashin jagorancin wanda ya kafa kuma Shugaba, Mista Martin-Mary Falana.
Tattaunawar a yayin zaman ta tabo batutuwan da suka shafi rayuwar yara da matasa a jihar, wadanda suka hada da yawaitar cin zarafin mata kamar lalata da fyade, cin zarafi a makarantu, kananan yara da auren dole, kaciyar mata, da kuma yawaitar shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasa.
Mahalarta taron sun amince da bukatar gaggawar samar da cikakken martani ta bangaren ilimi domin tunkarar wadannan kalubale.
Shugaban hukumar ya yi alkawarin ba da cikakken kudurin siyasa na hukumar tare da ba da tabbacin baiwa kungiyar K&TRC na NSUBEB goyon baya wajen samar da yanayi mai dacewa don samun nasarar aiwatar da aikin.
COV/Aliyu Muraki/Lafia.