Gwamnati Ta Jaddada ƙudirin Kare ‘Yancin Faɗin Albarkacin Baki Da ‘Yancin ‘Yan Jarida
Published: 21st, March 2025 GMT
Ya ce: “Ina so in sake nanata cewa Shugaban Ƙasa Tinubu, wanda yake cikakken ɗan dimokiraɗiyya, yana da niyyar kare ‘yancin ‘yan Nijeriya kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada. Haka zalika, yana ƙarfafa sukar gwamnati mai ma’ana da adawa tagari saboda suna da muhimmiyar rawa da suke takawa wajen ingantawa da zurfafa tsarin dimokiraɗiyyar mu.
“Ina kuma tabbatar da cewa wannan gwamnati za ta ci gaba da kare ‘yancin ‘yan jarida da samar da yanayi mai kyau ga aikin jarida a Nijeriya. Gwamnatin nan tana da yaƙinin cewa ‘yancin ‘yan jarida yana da muhimmanci wajen inganta nagartar shugabanci, gaskiya, da ci gaban ƙasa.”
Ministan ya yi amfani da damar taron don taya Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) murnar cika shekaru 70, yana mai bayyana wannan lokaci a matsayin wata babbar alama ta jajircewar su wajen kare ‘yancin ‘yan jarida da inganta aikin jarida.
Ya ce: “Ina kuma so in gode wa kafafen yaɗa labarai saboda jajircewar su wajen yaɗa muhimman batutuwan gwamnati. Wannan taro yana gudana a cikin wani lokaci mai muhimmanci, yayin da Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) take bikin cika shekaru 70. Wannan babbar alama ce da ke nuna yadda NUJ ke ci gaba da jajircewa kan ‘yancin ‘yan jarida da ingancin aikin jarida.”
Idris ya bayyana cewa Zauren Taron Bayani na Ministoci da ma’aikatar sa take jagoranta yana da manufar bai wa ‘yan Nijeriya damar samun cikakken bayani kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati, tare da jaddada ƙudirin gwamnati na nuna gaskiya da ɗaukar alhakin ayyukan ta.
“Wannan taro wata babbar dama ce ga ministoci su sanar da ‘yan Nijeriya irin cigaban da aka samu a ma’aikatun su. Ta wannan zauren tattaunawar, wanda aka inganta ta hanyar fasahohin zamani, muna tabbatar da ƙudirin mu na bayyana gaskiya da bayar da bayanai kai-tsaye dangane da manufofi, shirye-shirye, da sauye-sauyen da ke faruwa a ma’aikatun gwamnati.”
Ministan ya yaba wa Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, bisa ƙoƙarin sa na inganta martabar Nijeriya a idon duniya ta hanyar manufofin diflomasiyya da tsare-tsaren hulɗa da ƙasashen ƙetare.
Haka nan, ya jinjina wa Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, saboda irin sauye-sauyen da yake aiwatarwa domin daidaita ma’aikatar daidai da Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Tinubu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci wanda ya tattauna ta wayar tarho da jami’ar harkokin waje ta tarayyar turai ya bayyana cewa, ci gaba da tattaunawa a tsakanin Iran da Amurka ba shi da wata ma’ana, kamata ya yi jami’an tarayyar turai din su yi Allawadai da wuce gona da irin HKI akan Iran.
Da safiyar yau Asabar ne dai jami’ar diplomasiyyar ta turai Kaja Kallas ta kira yi minsitan harkokin wajen jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci inda su ka tattauna halin da ake ciki a yammacin Asiya da ya hada da harin da HKI ta kawo wa Iran.
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana harin na HKI da cewa, wuce gona da iri ne da keta hurumin kasar Iran, kuma harin da ta kai wa cibiyoyin Nukiliya ya yi sanadiyyar shahadar mutane da dama da su ka hada da malaman jami’oi , da kuma mata da kananan yara.
Ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su yi Allawadai da abinda HKI ta yi na take dokokin kasa da kasa.
Haka nan kuma ministan harkokin wajen na Jamhuriyar musulunci ta Iran ya yi ishara da cewa, kudurin da majalisar alkalai ta hukumar makamashin Nukiliyar Iran ta fitar akan Iran wanda kuma kasashe uku na turai tare da Amurka su ka gabatar da shi, shi ne ya bude wa ‘yan Sahayoniya mashigar da su ka yi amfani da ita wajen wuce gona da iri akan Iran.
A nata gefen babbar jami’ar diplomasiyyar tarayyar turai ta bayyana rashin jin dadinta akan abinda yake faruwa a cikin yankin na yammacin Asiya na rikice-rikice, tare da bayyana cewa suna goyon bayan aiki da diplomasiyya domin tabbatar da zaman lafiya.
A wani labarin mai alaka da wannan kasar Oman ta sanar da cewa, ba za a yi taron da aka shirya yi a tsakanin Iran da Amruka ba.
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Oman ce ta fitar da sanarwar cewa; Tattaunawar da aka shirya cewa za a yi a tsakanin Amurka da Iran ba za a yi ta ba a gobe Lahadi.
Ministan harkokin wajen na Oman ya kara da cewa; Diplomasiyya ce kadai ya kamata ta zama hanyar cimma zaman lafiya mai dorewa.