Ya ce: “Ina so in sake nanata cewa Shugaban Ƙasa Tinubu, wanda yake cikakken ɗan dimokiraɗiyya, yana da niyyar kare ‘yancin ‘yan Nijeriya kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada. Haka zalika, yana ƙarfafa sukar gwamnati mai ma’ana da adawa tagari saboda suna da muhimmiyar rawa da suke takawa wajen ingantawa da zurfafa tsarin dimokiraɗiyyar mu.

 

“Ina kuma tabbatar da cewa wannan gwamnati za ta ci gaba da kare ‘yancin ‘yan jarida da samar da yanayi mai kyau ga aikin jarida a Nijeriya. Gwamnatin nan tana da yaƙinin cewa ‘yancin ‘yan jarida yana da muhimmanci wajen inganta nagartar shugabanci, gaskiya, da ci gaban ƙasa.”

 

Ministan ya yi amfani da damar taron don taya Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) murnar cika shekaru 70, yana mai bayyana wannan lokaci a matsayin wata babbar alama ta jajircewar su wajen kare ‘yancin ‘yan jarida da inganta aikin jarida.

 

Ya ce: “Ina kuma so in gode wa kafafen yaɗa labarai saboda jajircewar su wajen yaɗa muhimman batutuwan gwamnati. Wannan taro yana gudana a cikin wani lokaci mai muhimmanci, yayin da Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) take bikin cika shekaru 70. Wannan babbar alama ce da ke nuna yadda NUJ ke ci gaba da jajircewa kan ‘yancin ‘yan jarida da ingancin aikin jarida.”

 

Idris ya bayyana cewa Zauren Taron Bayani na Ministoci da ma’aikatar sa take jagoranta yana da manufar bai wa ‘yan Nijeriya damar samun cikakken bayani kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati, tare da jaddada ƙudirin gwamnati na nuna gaskiya da ɗaukar alhakin ayyukan ta.

 

“Wannan taro wata babbar dama ce ga ministoci su sanar da ‘yan Nijeriya irin cigaban da aka samu a ma’aikatun su. Ta wannan zauren tattaunawar, wanda aka inganta ta hanyar fasahohin zamani, muna tabbatar da ƙudirin mu na bayyana gaskiya da bayar da bayanai kai-tsaye dangane da manufofi, shirye-shirye, da sauye-sauyen da ke faruwa a ma’aikatun gwamnati.”

 

Ministan ya yaba wa Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, bisa ƙoƙarin sa na inganta martabar Nijeriya a idon duniya ta hanyar manufofin diflomasiyya da tsare-tsaren hulɗa da ƙasashen ƙetare.

 

Haka nan, ya jinjina wa Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, saboda irin sauye-sauyen da yake aiwatarwa domin daidaita ma’aikatar daidai da Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Tinubu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya umarci sojoji su murƙushe ’yan ta’adda a faɗin Najeriya 

Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, ya umarci dakarun sojin Najeriya da su murƙushe ’yan ta’adda, masu tada ƙayar baya, da ’yan awaren Biyafara da ke barazana ga zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

Yayin bikin Ranar Sojoji ta 2025 da ya gudana a Jihar Kaduna, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima ya wakilci Shugaba Tinubu.

Mutum 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC

Tinubu ya ce: “Lokacin tashi ya yi. Ina tare da ku ɗari bisa ɗari don murƙushe masu yunƙurin rusa Najeriya. Ku ne ƙarfina, goyon bayana da addu’o’ina.”

Ya gargaɗi cewa barazanar da ake fuskanta ba ƙananan abubuwa ba ne.

“Waɗannan miyagun ba sa bambanta tsakanin coci da masallaci. Suna mayar da yara marayu ba tare da la’akari da ƙabila ko addini ba,” in ji shi.

Tinubu, ya kuma sha alwashin ci gaba da inganta walwalar sojoji da ba su kayan aiki na zamani.

“Za mu ci gaba da zuba jari a makamai, bayanan sirri da horo. Sojojinmu dole su kasance a shirye a koyaushe don kare Najeriya.”

Ya jinjina wa sojojin da suka rasa rayukansu wajen kare ƙasa.

“Jininsu ba zai zube a banza ba. Za mu ci gaba da tunawa da su har abada.”

Shugaban Hafsan Soji, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya yaba wa jarumtar dakarun sojin Najeriya.

“Karfinmu na gaske shi ne jarumta da sadaukarwar sojan Najeriya,” in ji shi.

Bikin ya ƙayatar da dandazon jama’a da manyan baƙi, inda aka nuna kayan aikin dakarun na zamani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai
  • TCN Ta Wayar Da Kan Al’ummomin Kaduna Kan Illar Lalata Kayan Wuta Da Gini Karkashen Babbar Wayar Wuta 
  • ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi
  • Kenya: Zanga-zanga Ta Tsayar Da Kai Komo A Birnin Nairobi
  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba
  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya
  •  Togo: An Yi Kiran Sake Yin Wata Sabuwar Zanga-zanagr Kin Jinin Gwamnati
  • Tinubu ya umarci sojoji su murƙushe ’yan ta’adda a faɗin Najeriya