Aminiya:
2025-11-03@06:53:39 GMT

Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu – Obasanjo

Published: 13th, March 2025 GMT

Tsohon shugaban Najeriya, Olusegun Obasanjo ya ce galibin ’yan Najeriya suna sha’awar yin amfani da muƙaman gwamnati ne kawai don arzuta kansu da abokan hulɗarsu su durƙusar da ƙasar fiye da yadda suka same ta.

Tsohon Shugaban ƙasar ya ce waɗannan mutane suna karɓar rancen biliyoyin Nairori, suna ganin cewa biyan kuɗaɗen gwamnati bayan an zaɓe su ba zai zama matsala ba.

Za a mayar da waɗanda Lakurawa suka raba da garuruwansu – Gwamnan Kebbi Peter Obi na ganawar sirri da gwamnan Bauchi

Obasanjo ya bayyana hakan ne a cikin sabon littafinsa mai suna ‘Nigeria: Past and Future’ inda ya zayyana halayen manyan shugabanni a matakin tarayya da na jihohi.

Littafin na ɗaya daga cikin sabbin littattafai guda biyu da aka ƙaddamar domin murnar cikar Obasanjo shekara 88 a makon jiya.

Tsohon Shugaban ƙasar ya ce akasarin waɗanda aka bai wa damar riƙe muƙaman shugabanci a ƙasar nan kamar Gwamnoni, shugabannin ƙasa, Ministoci, Kwamishinoni da shugabannin Ƙananan hukumomi, wasu nada mummunan shiri na son kai, kuma suna da yi niyyar azurta kansu ne yayin da al’ummar ƙasar ke ci gaba da durƙushewa cikin matsanancin talauci da rashin ci gaba.

Obasanjo ya ce, da yawa daga cikin waɗannan suna son zama gwamnoni ko kuma su jagoranci ƙasar nan ta wata hanya ko kuma wasu suna sha’awar yin amfani da ofisoshinsu ne kawai su arzuta kansu da abokan hulɗarsu sannan su bar ƙasar nan fiye da yadda suka same ta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana damuwarsa kan kalaman da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi game da Najeriya.

Kwankwaso, ya yi wannan magana ne bayan Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin yaƙi game da zargin kisan kiyashi da ake yi wa Kiristoci.

Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka

A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso, ya ce Najeriya ƙasa ce mai cikakken ’yanci, wadda ke fama da matsalar tsaro daga miyagu a sassa daban-daban na ƙasar.

“Matsalar tsaron da muke fuskanta ba ta bambanta tsakanin addini, ƙabila ko ra’ayin siyasa,” in ji shi.

Ya buƙaci gwamnatin Amurka da ta tallafa wa Najeriya da sabbin fasahohi domin yaƙar matsalar tsaro maimakon yin kalaman da za su iya raba kan ’yan ƙasa.

“Amurka ya kamata ta taimaka wa hukumomin Najeriya da ingantattun fasahohi don magance matsalolin tsaro, maimakon yin barazanar da za ta ƙara raba ƙasar,” in ji Kwankwaso.

Haka kuma, ya shawarci Gwamnatin Najeriya da ta naɗa jakadu na musamman domin inganta hulɗar diflomasiyya da Amurka da kare muradun ƙasar a matakin duniya.

Ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su zauna lafiya, inda ya bayyana cewa wannan lokaci ne da ya dace a fifita haɗin kan ƙasa ba abin da ke raba ta ba.

“Wannan lokaci ne da ya kamata mu mayar da hankali kan abin da zai haɗa kanmu ba wanda zai raba mu ba. Allah Ya albarkaci Najeriya,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare