Ayatullah Khatami: Tattaunawa Da Amurka Kaskanci Ne
Published: 7th, March 2025 GMT
Wanda ya jagoranci sallar juma’a a birnin Tehran ya bayyana cewa; Tattaunawa da Amurka kaskanci ne, ga shi kuwa al’ummar Iran tana da tunani ne irin na Ashura, ba ta karbar kaskanci.
Limamin na Tehran ya yi ishara da yadda duniya ta ga yadda Donald Trump ya wulakanta shugaban kasar Ukiraniya, don haka ya kamata masu dogaro da Amurka su kwana da sanin cewa, haka makomarsu za ta kasance, domin haka halayyar girman kai take.
Haka nan kuma limamin na Tehran ya ce; tare da cewa jagoran juyin musulunci na Iran ya sha jaddada cewa, babu aiki da tunani a cikin tattaunawa da Amurka, kuma ba abu ne na girma ba, sai dai kuma da akwai wadanda ba su nuna rashin jin dadinsu, to amma yanzu da su ka ga abinda ya faru da shugaban kasar Ukiraniya,sun amince da cewa tattaunawa da Amurkan ba abu ne da ya dace da mutumincin al’ummar Iran ba.
Dangane da barazanar kasashen Amurka, Fransa, Birtaniya da Jamus, akan aiki da kuduri mai lamba; 2231, Limamin na Tehran ya ce; Tun a tsawon shekaru 45 da su ka gabata ne wadannan kasashen suke maimaita magana daya, don haka babu wani alfanu da za su samu. Ayatullah Khatami ya kuma ce; Idan kuma wadannan kasashen ba su daina yi wa Iran baraza ba, to al’ummar Iran din za su yi maganinsu.
Da limamin ya tabo furucin ministan harkokin wajen Turkiya akan Iran, Ayatullah Khatami ya ce; Alakar Iran da makwabtanta ta ginu ne akan kyakkyawar makwabtaka, kuma Iran din ba ta da niyyar yin fada da makwabtanta, wannan shi ne abinda yake kunshe a cikin tsarin mulkin Iran.
Ayatullah Khatami ya kuma ce; Siyasar Turkiya a cikin wannan yankin tana cin karo da kyakkyawar makwabtaka, kuma ya kamata ‘yan siyasar Turkiya su fahimci cewa furucin da su ka yi akan Iran zai cutar da su.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar
Kakakin ofishi mai lura da harkokin yankin Taiwan a majalisar gudanarwar kasar Sin Chen Binhua, ya ce kalaman da aka jiyo jagoran yankin Taiwan na kasar Sin Lai Ching-te na yi dangane da sakamakon zagayen farko na kuri’ar kiranye da al’ummar Taiwan suka kada, ya nuna rashin gamsuwarsu da salon mulkin jam’iyyar DPP mai mulkin yankin.
Chen Binhua, wanda ya bayyana hakan ga manema labarai a Larabar nan, ya ce kalaman Lai na cike da yaudarar kai, sun kuma fayyace manufar da ya dage a kanta ta “neman ’yancin kan Taiwan”. Kazalika, mummunan kayen da DPP ta sha a kuri’un da aka kada ranar Asabar din karshen makon jiya, ya fayyace ajandarta ta yin fito-na-fito da Sin, tare da fafutukar neman ’yancin kan Taiwan, matakin da ya yi hannun riga da ra’ayoyin al’ummun Taiwan, kuma zai fuskanci turjiya daga akasarin al’ummun yankin na Taiwan. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp