Ayatullah Khatami: Tattaunawa Da Amurka Kaskanci Ne
Published: 7th, March 2025 GMT
Wanda ya jagoranci sallar juma’a a birnin Tehran ya bayyana cewa; Tattaunawa da Amurka kaskanci ne, ga shi kuwa al’ummar Iran tana da tunani ne irin na Ashura, ba ta karbar kaskanci.
Limamin na Tehran ya yi ishara da yadda duniya ta ga yadda Donald Trump ya wulakanta shugaban kasar Ukiraniya, don haka ya kamata masu dogaro da Amurka su kwana da sanin cewa, haka makomarsu za ta kasance, domin haka halayyar girman kai take.
Haka nan kuma limamin na Tehran ya ce; tare da cewa jagoran juyin musulunci na Iran ya sha jaddada cewa, babu aiki da tunani a cikin tattaunawa da Amurka, kuma ba abu ne na girma ba, sai dai kuma da akwai wadanda ba su nuna rashin jin dadinsu, to amma yanzu da su ka ga abinda ya faru da shugaban kasar Ukiraniya,sun amince da cewa tattaunawa da Amurkan ba abu ne da ya dace da mutumincin al’ummar Iran ba.
Dangane da barazanar kasashen Amurka, Fransa, Birtaniya da Jamus, akan aiki da kuduri mai lamba; 2231, Limamin na Tehran ya ce; Tun a tsawon shekaru 45 da su ka gabata ne wadannan kasashen suke maimaita magana daya, don haka babu wani alfanu da za su samu. Ayatullah Khatami ya kuma ce; Idan kuma wadannan kasashen ba su daina yi wa Iran baraza ba, to al’ummar Iran din za su yi maganinsu.
Da limamin ya tabo furucin ministan harkokin wajen Turkiya akan Iran, Ayatullah Khatami ya ce; Alakar Iran da makwabtanta ta ginu ne akan kyakkyawar makwabtaka, kuma Iran din ba ta da niyyar yin fada da makwabtanta, wannan shi ne abinda yake kunshe a cikin tsarin mulkin Iran.
Ayatullah Khatami ya kuma ce; Siyasar Turkiya a cikin wannan yankin tana cin karo da kyakkyawar makwabtaka, kuma ya kamata ‘yan siyasar Turkiya su fahimci cewa furucin da su ka yi akan Iran zai cutar da su.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
Daga Yusuf Zubairu Kauru
Al’ummar Karamar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna sun shiga halin kaka-ni-ka-yi duba da yadda rayukansu ke kasancewa cikin hadari yayin da suke gonakinsu.
A wata tattaunawa ta wayar tarho, wani jagoran matasa, Junaidu Ishaq, ya bayyana cewa kusan shekaru biyar ke nan da hare-haren ’yan bindiga ke ta faruwa akai-akai, wanda ya bar al’umma cikin fargaba da ƙuncin rayuwa.
Ya ce manoma suna shiga gonakinsu ne cike da fargaba domin komi na iya faruwa yayin da suke aiki a gonakin.
Mazauna yankin sun bayyana cewa Kauru, wadda aka fi sani da yawan gonaki da ke taka muhimmiyar rawa wajen samar da abinci a jihar Kaduna, yanzu manoma ba sa iya shiga gonakinsu cikin kwanciyar hankali saboda yadda ‘yan bindiga ke yawan kai musu hare-hare.
A koda yaushe iyayen yara suna fargaba kada ‘ya’yansu su yi nesa da su, yayin da iyalai da dama da ke fama da ƙangin talauci ke kara shiga cikin matsanancin hali.
Sun yi kira gwamnati da hukumomin tsaro su yi gaggawar kai ɗauki wanda zai bai wa manoman karkara kwarin gwiwa, waɗanda su ne ginshiƙin samar da abinci a yankin.
Mazaunan sun yi gargadin cewa idan ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba, hare-haren na iya haifar da ƙaruwar matsalar rashin abinci da yawaitar ƙaura daga yankin.
“Idan zuwa gona zai sa mutumya rasa ransa, to lalle akwai babban matsala,” in ji wani manomi a yankin.
Sun yi fatan cewa za a dawo da zaman lafiya a yankin, yadda ƙasar da Allah Ya albarkace su da ita za ta ci gaba da ciyar da al’ummar Kauru ba wurin binne su ba.