Ayatullah Khatami: Tattaunawa Da Amurka Kaskanci Ne
Published: 7th, March 2025 GMT
Wanda ya jagoranci sallar juma’a a birnin Tehran ya bayyana cewa; Tattaunawa da Amurka kaskanci ne, ga shi kuwa al’ummar Iran tana da tunani ne irin na Ashura, ba ta karbar kaskanci.
Limamin na Tehran ya yi ishara da yadda duniya ta ga yadda Donald Trump ya wulakanta shugaban kasar Ukiraniya, don haka ya kamata masu dogaro da Amurka su kwana da sanin cewa, haka makomarsu za ta kasance, domin haka halayyar girman kai take.
Haka nan kuma limamin na Tehran ya ce; tare da cewa jagoran juyin musulunci na Iran ya sha jaddada cewa, babu aiki da tunani a cikin tattaunawa da Amurka, kuma ba abu ne na girma ba, sai dai kuma da akwai wadanda ba su nuna rashin jin dadinsu, to amma yanzu da su ka ga abinda ya faru da shugaban kasar Ukiraniya,sun amince da cewa tattaunawa da Amurkan ba abu ne da ya dace da mutumincin al’ummar Iran ba.
Dangane da barazanar kasashen Amurka, Fransa, Birtaniya da Jamus, akan aiki da kuduri mai lamba; 2231, Limamin na Tehran ya ce; Tun a tsawon shekaru 45 da su ka gabata ne wadannan kasashen suke maimaita magana daya, don haka babu wani alfanu da za su samu. Ayatullah Khatami ya kuma ce; Idan kuma wadannan kasashen ba su daina yi wa Iran baraza ba, to al’ummar Iran din za su yi maganinsu.
Da limamin ya tabo furucin ministan harkokin wajen Turkiya akan Iran, Ayatullah Khatami ya ce; Alakar Iran da makwabtanta ta ginu ne akan kyakkyawar makwabtaka, kuma Iran din ba ta da niyyar yin fada da makwabtanta, wannan shi ne abinda yake kunshe a cikin tsarin mulkin Iran.
Ayatullah Khatami ya kuma ce; Siyasar Turkiya a cikin wannan yankin tana cin karo da kyakkyawar makwabtaka, kuma ya kamata ‘yan siyasar Turkiya su fahimci cewa furucin da su ka yi akan Iran zai cutar da su.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Jamhuriyar Nijar.
Mataimakin shugaban kasar na farko Mohammad-Reza Aref ya ce Iran na ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar da sauran kasashen nahiyar Afirka bisa tsarin juyin juya halin Musulunci.
Aref ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da ministan man fetur na kasar Nijar Sahabi Oumarou wanda ke Tehran, inda yake jagorantar wata tawaga, domin halartar taron hadin gwiwar tattalin arzikin Iran da Afirka karo na uku.
Ya ce da gaske ne gwamnatin Iran mai ci a yanzu tana son raya dangantakar da ke tsakaninta da kasashen Afirka ciki har da Nijar dangane da batutuwan da suka dace.
Ya kara da cewa, “Kasancewar manyan jami’an Nijar a taron da kuma kwamitin hadin gwiwa wani mataki ne mai ban sha’awa na inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.”
Mataimakin shugaban kasar ya jaddada cewa, bunkasa alaka da Nijar abu ne mai matukar muhimmanci, “idan aka yi la’akari da matsayinta kan ci gaban yanki da na kasa da kasa da kuma ra’ayi daya kan batutuwan Falasdinu da Lebanon.”
A yayin da yake tsokaci ga kiran da ministan na Nijar ya yi na inganta alaka a fannin noma, man fetur, da makamashi mai dorewa, Aref ya bayyana wadannan fannoni guda uku a matsayin muhimman batutuwan da suka shafi dangantakar Iran da Nijar, wadanda ya ce kwamitin hadin gwiwa zai duba su.
Yayin da yake tsokaci kan dangantakar tattalin arziki, ya ce, ya kamata kamfanoni masu zaman kansu na kasashen biyu su zuba jari don ciyar da matakin hadin gwiwa zuwa matsayi mafi girma.