Damuwar IMF akan kalubalen tattalin arzikin Najeriya yaudara ne – Farfesa Yushau Ango
Published: 7th, March 2025 GMT
Damuwar IMF akan kalubalen tattalin arzikin Najeriya yaudara ne – Farfesa Yushau AngoWani masani kan harkokin kudi, Farfesa Yushau Ibrahim Ango, ya ce damuwar da asusun lamuni na duniya IMF ke yi kan kalubalen tattalin arzikin da kasar ke fuskanta a halin yanzu yaudara ce.
Farfesa Yushau Ango ya bayyana haka ne a wata hira da aka yi da shi a Kaduna.
Ya kuma jaddada bukatar hukumar ba da lamuni ta duniya IMF ta gabatar da shawarwari masu inganci don magance kalubalen da ke haifar da cire tallafin man fetur, wanda manufofinsa suka yi tasiri.
Masanin harkokin kudi ya bayyana raguwar farashin kayan abinci a matsayin na wucin gadi sai dai idan ba a samar wa manoman kasar nan abubuwan da suka dace da suka hada da taki mai rahusa domin bunkasa noma.
Farfesa Yushau Ango ya kuma yi nuni da cewa, rage farashin man da wasu kamfanonin mai ke yi, ana sa ran zai sa masu ababen hawa za su samu saukin amfani da man.
Ya kuma yi kira da a samar da dorewar manufofin tattalin arziki domin kiyaye ka’idojin mulkin dimokuradiyya.
COV/ SULEIMAN KAURA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Farfesa Yushau Ango
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba
Kwanan baya, kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya shirya taron bita tare da wadanda ba ’yan jam’iyyar ba, dangane da yanayin tattalin arzikin kasar, da kuma ayyukan tattalin arziki da za a aiwatar a rabin shekarar bana ta biyu, domin sauraren ra’ayoyinsu.
Xi Jinping, babban sakataren jam’iyyar ne ya shugabanci taron tare da ba da muhimmin jawabi, inda ya ce, dole ne a zage damtse wajen gudanar da ayyukan tattalin arziki a rabin shekarar bana ta biyu, kuma a tabbatar da gudanar da ayyukan ba tare da tangarda ba, kana a aiwatar da cikakken sabon tunanin raya kasa daga dukkan fannoni, da gaggauta kafa tsarin raya kasa, da kiyaye aiwatar da manufofi ba tare da matsala ba, da inganta aiwatar da manufofi tare da yin hangen nesa da sanin ya kamata.
Shugaban na Sin ya ce, ya zama wajabi a mayar da muhimmanci ga samar da guraben aikin yi, da kwantar da hankulan kamfanoni, da tafiyar da harkokin kasuwanci, da samar da tabbaci game da hasashen da ake yi kan tattalin arziki, da karfafa sayayya, da dakatar da yin takara maras dacewa, da kawar da cikas a kasuwar gida, da rungumar wani sabon tsarin ci gaba mai “zagaye biyu”, wato wanda zai tanadi amfani da kasuwar gida a matsayin jigo, tare da barin kasuwannin gida da na waje su karfafi junansu, a kokarin cimma manufar raya tattalin arziki, da zamantakewar al’ummar kasar a bana, da samun nasarar kammala shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 14. (Tasallah Yuan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp