Leadership News Hausa:
2025-08-02@02:16:41 GMT

Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi

Published: 7th, March 2025 GMT

Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi

Bayan da Amurka ta sanar da sanya karin haraji, kasashen Canada da Mexico da ma Sin dukkan sun dauki matakan ramuwar gayya. A ranar 4 ga wata, bi da bi ne ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin da ma kwamitin kula da dokokin harajin kwastan na majalisar gudanarwar kasar sun sanar da jerin matakai na tinkarar matakan haraji na Amurka.

Kakakin ma’aikatar wajen kasar Sin ya kuma jaddada cewa, nuna fin karfi ba shi da amfani da kasar Sin, kuma matsawa da barazana ba hanya ce ta cudanya da kasar. Hakikanin abubuwan da suka faru a shekarun baya ma sun shaida yadda kasar Sin ke mai da matsawa da aka yi mata a matsayin karfin da ke sa ci gabanta, bisa ga juriyar masana’antunta da kirkire-kirkiren fasahohi da ma hadin gwiwarta da sassa daban daban, har ma ta yi ta murkushe makircin Amurka.

 

A hakika, al’ummar kasar Amurka suna sane da me matakan haraji da Trump ya dauka za su haifar musu. Kamar yadda wani dan kasar ya ce, “idan an samu hauhawar farashi na kaso 25%, mu kanmu ne za mu biya kudin, a maimakon gwamnati ko mutanen kasar Mexico.” Abin hakan yake, duk da cewa matakin haraji ya lalata dokokin cinikin kasa da kasa tare da haifar da rashin tabbas ga farfadowar tattalin arzikin duniya, amma daga karshe, kamfanonin kasar Amurka da ma al’ummar kasar ne za su dandana kudarsa. Daidai kamar yadda Ben Ayers, masanin ilmin tattalin arziki na kasar Amurka ya ce, “Karin iyalai a Amurka za su kara kimtsa wa shiga yanayin tattalin arziki mara tabbas da za su fuskanta a shekarar 2025.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da aniyar ta ta bunƙasa harkar kiwon dabbobi a Nijeriya a matsayin wata muhimmiyar hanya ta magance rikice-rikicen da ke tsakanin manoma da makiyaya, tare da amfani da damar tattalin arzikin da ke cikin ɓangaren.

Ɗaya daga cikin Shugabannin Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gyaran Harkar Kiwo, Farfesa Attahiru Jega, shi ne ya bayyana hakan a wurin taron tattaunawa tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa, wanda Gidauniyar Sa Ahmadu Bello ta shirya a Kaduna, a ranar Laraba.

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar

Jega ya bayyana cewa sabuwar Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo tana ɗaya daga cikin ginshiƙan da ke cikin shirin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na sauya fasalin ɓangaren kiwon dabbobi.

Ya jaddada cewa ana aiwatar da hangen nesa na Shugaban Ƙasa ba tare da son rai na siyasa ba, tare da mayar da hankali kan haɗa kai da duk masu ruwa da tsaki, ciki har da gwamnatocin jihohi, sarakunan gargajiya, al’ummomin makiyaya da sauran muhimman masu ruwa da tsaki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka
  • Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • ’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina