Gwamnatin jihar Kebbi, ta kaddamar da rabon kayayyakin noman rani da kayan abinci na watan Ramadan ga manoma da al’ummar jihar, inda ta umurci jami’an tsaro da su kama duk wanda aka samu yana sayar da kayan abinci da na aikin noma.

A jawabinsa yayin kaddamar da rabon, gwamnan jihar, Kwamared Nasir Idris ya bayyana cewa, matsakaitan manoma 200,000 a fadin kananan hukumomin jihar 21 ne za su ci gajiyar shirin.

Gwamnan ya bayyana cewa, samar da kayan aikin gona ga manoma zai taimaka wajen bunkasa samar da abinci a jihar.

Ya yi kira ga shugabannin addini da na al’umma da kuma jami’an gwamnati da ke da alhakin rabon kayayyakin, da su tabbatar da an yi adalcin wajen  rabon kayayyakin.

Ministan noma da samar da abinci, Abubakar Kyari, ya ce shugaba Bola Tinubu, yana bakin kokarinsa wajen inganta harkar noma, ta hanyar karfafa gwiwar kowane bangare na al’umma da su ba da muhimmanci ga shirin noma na gwamnati.

Ya ce, rabon kayayyakin amfanin gona ga manoma a jihar Kebbi shi ne don bunkasa ayyukan noman rani a shekarar 2025, domin kara yawan kayan abinci a jihar da kuma dakile matsalar karancin abinci.

Kwamishinan noma na jihar Alhaji Shehu Mu’azu ya ce gwamnatin jihar ta dukufa wajen inganta kayan noma da kuma dakile matsalar karancin abinci.

Ya ce, matakin da gwamnati ta dauka shi ne rage wa manoma wahalhalu a lokacin noman rani tare da rage radadin da talakawa ke fuskanta a cikin watan Ramadan.

Kayayyakin da aka bayar sun hada da injinan wutar lantarki guda 3000, da famfo mai amfani da hasken rana guda 10,000, da famfunan ruwa na LPG guda 5000, da injin feshin maganin kwari guda 10,000 da dai sauransu.

Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Noman Rani rabon kayayyakin

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.

Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.

Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen  tsaro.

CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda