Gwamnatin Kebbi Ta Sha Alwashin Kawar Da Matsalar Abinci A Jihar
Published: 7th, March 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kebbi, ta kaddamar da rabon kayayyakin noman rani da kayan abinci na watan Ramadan ga manoma da al’ummar jihar, inda ta umurci jami’an tsaro da su kama duk wanda aka samu yana sayar da kayan abinci da na aikin noma.
A jawabinsa yayin kaddamar da rabon, gwamnan jihar, Kwamared Nasir Idris ya bayyana cewa, matsakaitan manoma 200,000 a fadin kananan hukumomin jihar 21 ne za su ci gajiyar shirin.
Gwamnan ya bayyana cewa, samar da kayan aikin gona ga manoma zai taimaka wajen bunkasa samar da abinci a jihar.
Ya yi kira ga shugabannin addini da na al’umma da kuma jami’an gwamnati da ke da alhakin rabon kayayyakin, da su tabbatar da an yi adalcin wajen rabon kayayyakin.
Ministan noma da samar da abinci, Abubakar Kyari, ya ce shugaba Bola Tinubu, yana bakin kokarinsa wajen inganta harkar noma, ta hanyar karfafa gwiwar kowane bangare na al’umma da su ba da muhimmanci ga shirin noma na gwamnati.
Ya ce, rabon kayayyakin amfanin gona ga manoma a jihar Kebbi shi ne don bunkasa ayyukan noman rani a shekarar 2025, domin kara yawan kayan abinci a jihar da kuma dakile matsalar karancin abinci.
Kwamishinan noma na jihar Alhaji Shehu Mu’azu ya ce gwamnatin jihar ta dukufa wajen inganta kayan noma da kuma dakile matsalar karancin abinci.
Ya ce, matakin da gwamnati ta dauka shi ne rage wa manoma wahalhalu a lokacin noman rani tare da rage radadin da talakawa ke fuskanta a cikin watan Ramadan.
Kayayyakin da aka bayar sun hada da injinan wutar lantarki guda 3000, da famfo mai amfani da hasken rana guda 10,000, da famfunan ruwa na LPG guda 5000, da injin feshin maganin kwari guda 10,000 da dai sauransu.
Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Noman Rani rabon kayayyakin
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.