Kebbi Ta Kashe Naira miliyan 67 Wajen Biya Sadakin Ma’aurata 300
Published: 28th, February 2025 GMT
Shugaban jam’iyyar APC na kasa kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ne ya tsaya a matsayin wakilin na angwaye yayin da Mai martaba Sarkin Gwandu, Manjo Janar Muhammad Iliyasu Bashar murabus ne ya tsaya a matsayin wakilin na amaren.
Gwamna Nasir Idris, yayin da yake godewa uwargidansa Hajiya Nafisa Nasir Idris bisa wannan shiri a karkashin gidauniyarta ta “Asusun NANAS ”, ya yi alkawarin bayar da goyon baya da kuma ci gaba da gudanar da shirin na shekara-shekara domin amfanin al’ummar Kebbi, ya kuma shawarci ma’auratan da su kasance masu adalci da mutunta ra’ayin juna.
Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Sanata Abubakar Atiku-Bagudu, ya bayyana taron a matsayin tunatarwa ga daidaikun mutane a cikin al’umma da su rika duba kansu tare da tambayar kansu nawa suka taimaka wajen yin aure a yankunansu.
Shima da yake jawabi, sakataren jam’iyyar APC na kasa, Dr Tajuddeen Bashiru, ya lura cewa, ma’auratan ba aure kadai suke yi ba, har ma gwamnatin jihar ta basu karfin gwiwa.
Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar Kebbi ba wai kawai ta aurar da ma’aurata 300 ba, amma tana baiwa iyalai 300 damar dogaro da kai.
Gwamnatin jihar Kebbi, ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na ware naira miliyan 54 na sadakin ma’aurata 300, kayan daki, kayan abinci da duk wani nauyin da ya rataya a wuyan aure in ban da wurin kwana.
Sheik Aminu Ibrahim Daurawa, Sheik Professor Mansur Sokoto, Sheik Professor Mansur Isa da Sheik AbdurRahman Isa-Jega na daga cikin malaman addinin musulunci da suka shaida bikin.
COV/Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122
Hukumar dake kula da ‘yan hijira dake karkashin MDD ta sanar da cewa, mutanen yake-yake da rikice-su ka tilastawa yin hijira a duniya ya kai miliyan 122.
A yau Alhamis ne dai hukumar dake kula da ‘yan hijirar ta bayyana haka, tana kai kara da cewa; gajiyawar da aka yi na warware fadace-fadace da rikicen da suke faruwa a duniya ne su ka kara yawan ‘yan hijirar, daga ciki har da kasashen Sudan da kuma Ukiraniya.
Haka nan kuma ta ce; Tun daga 2015 ne ake samun koma baya na kudaden da ya kamata a rika bayarwa domin taimakawa ‘yan hijira.
Shugaban hukumar ‘yan hijirar ta MDD Filippo Grandi wanda ya gabatar da rahoto akan halin da ake ciki, ya yi ishara da cewa, tun daga watan Aprilu na wannan shekara ta 2025 da ake ciki an sami karuwar mutane miliyan biyu da su ka zama ‘yan hijira, duk da cewa wani adadin da ya kai mutane miliyan biyu ‘yan kasar Syria sun koma kasarsu bayan faduwar gwamnatin Basshar Asad.
Filippo Grandi ya ce rikice-rikicen kasar Myanmar, da yakin Ukiraniya da Sudan su ne ummul-haba’isin karuwar ‘yan hijirar da kuma gajiyawa wajen kawo karshen hakan.
Kasar Amurka tana cikin wadanda su ka rage yawan taimakon kudaden da suke bayarwa a harkar agaji, yayin da kasashe kamar Birtaniya da wasu kasashen turai suke bayar da kadan.