Kebbi Ta Kashe Naira miliyan 67 Wajen Biya Sadakin Ma’aurata 300
Published: 28th, February 2025 GMT
Shugaban jam’iyyar APC na kasa kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ne ya tsaya a matsayin wakilin na angwaye yayin da Mai martaba Sarkin Gwandu, Manjo Janar Muhammad Iliyasu Bashar murabus ne ya tsaya a matsayin wakilin na amaren.
Gwamna Nasir Idris, yayin da yake godewa uwargidansa Hajiya Nafisa Nasir Idris bisa wannan shiri a karkashin gidauniyarta ta “Asusun NANAS ”, ya yi alkawarin bayar da goyon baya da kuma ci gaba da gudanar da shirin na shekara-shekara domin amfanin al’ummar Kebbi, ya kuma shawarci ma’auratan da su kasance masu adalci da mutunta ra’ayin juna.
Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Sanata Abubakar Atiku-Bagudu, ya bayyana taron a matsayin tunatarwa ga daidaikun mutane a cikin al’umma da su rika duba kansu tare da tambayar kansu nawa suka taimaka wajen yin aure a yankunansu.
Shima da yake jawabi, sakataren jam’iyyar APC na kasa, Dr Tajuddeen Bashiru, ya lura cewa, ma’auratan ba aure kadai suke yi ba, har ma gwamnatin jihar ta basu karfin gwiwa.
Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar Kebbi ba wai kawai ta aurar da ma’aurata 300 ba, amma tana baiwa iyalai 300 damar dogaro da kai.
Gwamnatin jihar Kebbi, ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na ware naira miliyan 54 na sadakin ma’aurata 300, kayan daki, kayan abinci da duk wani nauyin da ya rataya a wuyan aure in ban da wurin kwana.
Sheik Aminu Ibrahim Daurawa, Sheik Professor Mansur Sokoto, Sheik Professor Mansur Isa da Sheik AbdurRahman Isa-Jega na daga cikin malaman addinin musulunci da suka shaida bikin.
COV/Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026
Gwamnatin Jihar Gombe ta ƙaddamar da taron sauraron ra’ayoyi jama’a kan shirye-shiryen tsara kasafin kuɗin shekarar 2026 a wani yunƙuri na jaddada ƙudirinta na gudanar da mulki cikin gaskiya da haɗin kai.
Da yake jawabi a wajen taron, Mataimakin Gwamnan Jihar, Dakta Manassah Daniel Jatau, ya bayyana cewa wannan mataki na nuna jajircewar Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya wajen tabbatar da cewa ra’ayoyin jama’a na taka muhimmiyar rawa a tsara kasafin kuɗi da aiwatar da shi.
Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti Gobara ta tashi a babban kanti a AbujaYa ce tattaunawar ta bai wa gwamnati damar haɗa kai da sarakunan gargajiya, mata, matasa, ƙungiyoyin farar hula da sauran masu ruwa da tsaki, domin bayar da shawarwari kan muhimman fannoni kamar ilimi, lafiya, noma da gine-gine, da za su amfanar da al’umma baki ɗaya.
Dakta Jatau ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta samu ci gaba wajen alkinta kuɗaɗe cikin tsari da gaskiya, wanda hakan ya sa Gombe ke samun matsayi mai kyau a ɓangaren ingantaccen gudanar da kuɗi da sauƙin kasuwanci a Najeriya.
“Kasafin kuɗin 2026 zai mai da hankali ne kan ci gaba da ayyukan da ake yi, tare da ƙara zuba jari a muhimman fannoni, da tabbatar da daidaito da manufofin ci gaban ƙasa da na duniya,” in ji shi.
A nasa ɓangaren, Kwamishinan Kasafi da Tsare-Tsaren Tattalin Arziki, Alhaji Salihu Baba Alkali, ya bayyana taron a matsayin wata hanya ta buɗe ƙofa tsakanin gwamnati da jama’a domin samun fahimta da amincewa.
Ya buƙaci mahalarta taron da su bayar da shawarwari masu amfani da za su taimaka wajen samar da kasafin kuɗin da zai kasance mai ɗorewa kuma mai amfani ga kowa da kowa.
Kwamishinan ya kuma gode wa mahalartan bisa yadda suka bayar da gudunmawa, yana mai tabbatar da cewa za a yi la’akari da shawarwarinsu a cikin tsarin ƙarshe na kasafin kuɗin jihar.