Aminiya:
2025-06-15@14:39:29 GMT

Kotu ta hana Gwamnatin Tarayya riƙe kuɗin ƙananan hukumomin Kano

Published: 17th, February 2025 GMT

Wata Babbar Kotun Jihar Kano ta haramta wa Gwamnatin Tarayya riƙewa ko kuma yi wa kuɗaɗen ƙananan hukumomi 44 na jihar katsalandan.

Mai Shari’a Musa Ibrahim Muhammad ne ya yanke hukuncin a ranar Litinin, biyo bayan ƙarar da wakilan ƙananan hukumomin jihar suka kai na kare ‘yancinsu na cin gashin kai dangane da kuɗaɗen da Gwamnatin Tarayyar ke ware musu.

Mutum biyu sun shiga hannu kan yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Yobe Gwamnati ta raba wa mata tallafin awakai na N5bn a Katsina

Wannan shari’ar dai ta samo asali ne bayan da jam’iyyar adawa ta APC ta nemi kotu da ta dakatar da bai wa ƙananan hukumomin jihar kuɗaɗe, bisa zargin tafka maguɗi a zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a watan Oktoban 2024.

Aminiya ta ruwaito cewa, Shugaban  Jam’iyyar APC na Kano, Abdullahi Abbas ne ya jagoranci shigar da ƙarar wadda take ƙalubalantar wasu hukumomin Gwamnatin Tarayya da suka haɗa da Babban Bankin Nijeriya (CBN), Asusun Raba Kuɗi na Tarayya (FAAC), da kuma dukkan ƙananan hukumomi 44 na Kanon.

Sai dai kuma hukuncin da babbar kotun Kano ta yanke ya tabbatar da haƙƙin ƙananan hukumomi na karɓar kudadtensu, tare da hana gwamnatin tarayya ko wasu hukumominta riƙe kuɗaɗen .

A watan Nuwambar bara ce dai Shugaban Ƙungiyar Ƙananan Hukumomi, Ibrahim Muhammad ya jagoranci tawagar masu shigar da ƙara ta hannun lauyansu, Bashir Yusuf Muhammad, suna neman kotun ta hana riƙewa ko jinkirin sakin kuɗin ƙananan hukumomin jihar.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Jihar Kano Kuɗin Ƙananan Hukumomi Gwamnatin Tarayya

এছাড়াও পড়ুন:

Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe, ta tabbatar da mutuwar mutum biyar da kuma jikkatar wasu 13, sakamakon tashin wutar lantarki a unguwar Tudun-Wada, Pantami a jihar.

Wutar ta tashi ne da safiyar ranar Asabar sakamakon matsala da ta taso daga wata tiransifoma a yankin, kamar yadda kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana.

Sojoji sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa

Cikin waɗanda suka rasa rayukansu har da Babban Sakatare na Ma’aikatar Ayyuka ta Musamman ta jihar, Alhaji Muhammad Yusuf Kulani, tare da ’ya’yansa da wasu mazauna unguwar.

Marigayin shi ne shugaban ƙungiyar ƙwararrun akantoci ta Jihar Gombe (ANAN).

’Yan sanda daga ofishin Low-Cost sun isa wajen don tabbatar da tsaro da kuma kai waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Bello Yahaya, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan.

Ya kuma ce za su gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin tashin wutar da kuma ɗaukar matakan kare faruwar hakan a gaba.

Ya kuma roƙi al’umma da su kasance masu bin doka tare da bayar da haɗin kai yayin gudanar da binciken.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2