Sallah: ’Yan sanda sun yi alƙawarin tabbatar da tsaro a Gombe
Published: 5th, June 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta shirya tsare-tsaren tsaro domin ganin an yi Sallar Idi cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya.
Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa za a tura ’yan sanda da sauran jami’an tsaro zuwa filayen Idi, Masallatai, da wuraren taro domin kula da tsaro da zirga-zirgar jama’a.
Za a sanya ido sosai a manyan hanyoyi musamman waɗanda ke kai wa zuwa wuraren sallah, domin rage cunkoso da sauƙaƙa zirga-zirgar jama’a.
An ware ƙofofin shiga da fita a filayen Sallah domin a riƙa duba mutane da kayan da suke ɗauke da su.
Rundunar ta kuma roƙi jama’a da su bi waɗannan ƙa’idoji domin kauce wa jinkiri.
’Yan sandan sun gargaɗi mutane da ka da su ajiye motoci ba bisa ƙa’ida ba, sannan su kaucewa yin salla a tsakiyar hanya, ko toshe hanyoyin fita.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, ya roƙi mutane da su bayar da haɗin kai wajen bin doka, tare da kasancewa masu lura da duk wani abu da zai kawo barazana.
Ya kuma gargaɗi masu laifi da su guji duk wani abu da zai jawo tashin hankali a jihar.
Hakazalika, ya taya al’ummar Gombe murnar Sallar Idi, tare da tabbatar musu cewa ’yan sanda za su ci gaba da kare lafiyar jama’a domin a yi bukukuwan sallah cikin kwanciyar hankali.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Ministan ya bayyana gabatarwar da C-WINS ta yi a matsayin mai motsa zuciya kuma mai cike da ƙarin haske.
Ya ce: “A yau na koyi abubuwa da dama. Yawancin ’yan Nijeriya, kamar ni kai na, sun san cutar masassarar cizon sauro amma ba su san da ƙyandar jamus da mummunan tasirin ta ba.
“Gaskiya batun cewa za a iya haihuwar yara makafi, kurame ko kuma masu nakasar zuciya sakamakon kamuwa da ƙyanda daga uwa a lokacin ɗaukar ciki babbar masifa ce da ya kamata mu haɗa kai mu daƙile ta.”
Ya ƙara da cewa ma’aikatar za ta haɗa hannu da sauran hukumomin da suka dace wajen tsara saƙonnin faɗakarwa da shirye-shiryen ilimantar da al’umma.
Ya kuma shawarci tawagar da su nemi haɗin kan Majalisar Tarayya domin samun cikakken goyon baya na doka.
Ya ce: “Ba ma so wannan zama ya tsaya nan kawai. Mu mayar da wannan haɗin gwiwa abin da zai ɗore, mai amfani, kuma mai faɗi da tasiri. Rigakafi ya fi magani — kuma wannan fannin ne inda bayani ke ceton rayuka ainun.”
A cikin nata jawabin, jagorar tawagar C-WINS, Dakta Nihinlola Mabogunje, ta jaddada gaggawar wayar da kan jama’a kafin lokacin fara kamfen ɗin.
Ta gabatar da cikakken bayani kan muhimmancin rigakafin daga cututtukan ƙyandar jamus fata, musamman a matsayin da Nijeriya ke da shi wajen yawaitar waɗannan cututtuka.
Dakta Mabogunje ta bayyana cewa Nijeriya tana da kusan kashi 20 cikin ɗari na dukkan cututtukan ƙyandar da ake samu a duniya, inda yankin Arewa-maso-gabas yake ɗauke da fiye da kashi 60 cikin ɗari na waɗanda abin ya shafa a ƙasar nan.
Dangane da ƙyandar jamus, ta bayyana cewa cutar tana barazana musamman ga mata masu juna biyu, domin kamuwa da cutar a watannin farko na ɗaukar ciki yana iya janyo haihuwar jarirai masu nakasa kamar makanta, kurmancewa ko lalacewar zuciya.
Ta tabbatar da cewa rigakafin da za a yi amfani da shi yana da inganci kuma ba shi da wani haɗari ga lafiyar mutum, tana mai cewa tun tuni ake amfani da shi, fiye da shekaru 50 a duniya, kuma ya ceci rayuka sama da miliyan 94.
Ta kuma yaba da aikin Hukumar NAFDAC wajen tantancewa da amincewa da rigakafin domin amfani da shi a Nijeriya.
Ta roƙi Gwamnatin Tarayya da ta jagoranci faɗakarwar a matakin ƙasa domin kawar da ji-ta-ji-ta da ƙarfafa gwiwar jama’a.
Likita Mabogunje ta ce: “Don cimma burin kashi 95 na yawan masu karɓar rigakafi, muna buƙatar saƙonnin da suka dace, masu sahihanci da kuma daidaito, waɗanda za a isar ta hanyoyin da ’yan Nijeriya suke yawan dogaro da su a kullum.”
A martanin sa, Minista Idris ya umurci jami’an sashen sadarwa na ma’aikatar sa da su yi aiki tare da C-WINS domin ƙirƙirar kayan faɗakarwa da suka dace da al’adun jama’a, waɗanda za a yaɗa ta kafafen watsa labarai na gwamnati da masu zaman kan su a dukkan faɗin ƙasar nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp