HausaTv:
2025-06-06@07:38:55 GMT

Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa Wadanda Suke Jin Yunwa A Gaza

Published: 4th, June 2025 GMT

Gwamnatin kasar Amurka wacce ta bude cibiyoyin rarraba kayakin Agaji a Gaza, ta ce zata rufe cibiyoyin zuwa ranar Alhamis mai zuwa don sake tsara ayyukan Rabomn.  Majiyar gwamnatin Amurka ta bayyana cewa ta dauki wannan matakin ne saboda sojojin yahudawan suna kashe falasdinawa wadanda suke fama da yunwa a lokacinda suka iso cibiyoyin raba abincin ko kuma suka hau kan hanyar zuwa karban abincin.

Labarin ya kara da cewa a jiya Talata kadai sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa mayunwata 27 a kokarinsu na karban abinci.

Sannan a yau Laraba ya zuwa lokacin bada wannan labarin sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa 32 a hare-haren da suka kai kan yankuna daban-daban a Gaza.

Majiyar ta kara da cewa Palasdinawa 95 ne sojojin yahudawan suka kai ga shahada a cikin sa’o’I 24 da suka gabata a gaza, sannan wasu 440 kuma suka ji rauni.

Tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 ya zuwa yanzu Falasdina 54,607 ne suka yi shahada a Gaza, kuma tana ci gaba da kara kashewa ba wanda ya isa ya yi magana a duniya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin yahudawan

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi

Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila suna da mugun nufi kan Iran da kasashen musulmi

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila na da mugun nufi kan Iran da kasashen musulmi.

A yayin wani jawabi da ta gabatar a wajen juyayin tunawa da rasuwar Imam Khumaini {r.a}, Pezeshkian ya ce: Haramtacciyar kasar Isra’ila ba za ta iya aikata wani aiki hauka da wauta ba, idan kasashen musulmi suka hada kansu.

Pezeshkian ya kara da cewa: Wadanda ke da’awar kare hakkin bil’adama suna kare “haramtacciyar kasar Isra’ila” mai laifi, kuma suna ci gaba da adawa da shirin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Ya ci gaba da cewa: “Babu mutum mai ‘yanci da zai yarda da zalunci da girman kai, kuma Iran ba zata yarda da shi ba.”

Pezeshkian ya bayyana cewa: “Za su dakile duk wani makirce-makircen abokan gaba kuma ba za su taba yin watsi da ‘yancinsu na nukiliya da na kimiyya ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano
  • Shugaban Kasar Rasha Vladimir Putin Zia Kawo Ziyara Tehran Nan Kusa
  • Mahajjata Aikin Hajjin Bana Sun Tafi Tsayiwar Arafat A Yau Alhamis Don Fara Ginshikin Aikin Hajj
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ben Gurion Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
  • Zulum Ya Yabawa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima
  • Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Wani Kisan Kiyashi Kan Masu Bukatar Kayan Agaji