HausaTv:
2025-07-23@22:55:16 GMT

Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa Wadanda Suke Jin Yunwa A Gaza

Published: 4th, June 2025 GMT

Gwamnatin kasar Amurka wacce ta bude cibiyoyin rarraba kayakin Agaji a Gaza, ta ce zata rufe cibiyoyin zuwa ranar Alhamis mai zuwa don sake tsara ayyukan Rabomn.  Majiyar gwamnatin Amurka ta bayyana cewa ta dauki wannan matakin ne saboda sojojin yahudawan suna kashe falasdinawa wadanda suke fama da yunwa a lokacinda suka iso cibiyoyin raba abincin ko kuma suka hau kan hanyar zuwa karban abincin.

Labarin ya kara da cewa a jiya Talata kadai sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa mayunwata 27 a kokarinsu na karban abinci.

Sannan a yau Laraba ya zuwa lokacin bada wannan labarin sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa 32 a hare-haren da suka kai kan yankuna daban-daban a Gaza.

Majiyar ta kara da cewa Palasdinawa 95 ne sojojin yahudawan suka kai ga shahada a cikin sa’o’I 24 da suka gabata a gaza, sannan wasu 440 kuma suka ji rauni.

Tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 ya zuwa yanzu Falasdina 54,607 ne suka yi shahada a Gaza, kuma tana ci gaba da kara kashewa ba wanda ya isa ya yi magana a duniya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin yahudawan

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu

Sojojin Yemen sun kai hari kan filin tashi da saukar jiragen sama na Lod da makami mai linzami nau’in ‘Palestine 2’

Dakarun sojin Yemen sun sanar da aiwatar da wani harin soji na musamman da aka kai kan tashar jirgin saman Lod da ke yankin Jaffa da aka mamaye da makami mai linzami kirar “Palestine 2”.

A cikin wata sanarwa da ta fitar da yammacin jiya, Rundunar Sojin Yemen ta bayyana cewa: Farmakin ya sanya miliyoyin garken yahudawan sahayoniyya tsere zuwa matsuguni karkashin kasa tare da dakatar da ayyukan tashar jirgin sama.

Sanarwar ta ce harin da aka kaiwa filin jirgin sama na Lod nasara ce ga al’ummar Falastinu da ake zalunta da kuma mujahidansu, da kuma mayar da martani ga kisan kiyashin da yahudawan sahayoniyya suka yi a zirin Gaza.

Sanarwar ta yi kira ga daukacin al’ummar Larabawa da na Musulunci da su fito kan tituna “don nuna goyon bayansu ga ‘yan uwansu a Gaza, saboda yadda suke fuskantar zalunci da wuce gona da iri na killacewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
  •  Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki
  • A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24
  • Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
  • Yahudawan Sahayoniyya Sun Bullo Da Dabarar Kisa Kan Falasdinawa Musamman ‘Yan Gudun Hijira
  • WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza
  • Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne