Leadership News Hausa:
2025-06-02@10:05:38 GMT

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

Published: 1st, June 2025 GMT

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

Ta hanyar da za ki gano kuwa ita ce, ki kai mata ziyara ta wuni daya kuma idan kin je ki kula da yaya yanayin huldodinta da kuma gyaran jikinta suke a cikin gidanta, ta nan ne za ki fahimci matsalar rashin jituwarta da mijin na ta.

Domin ita matsalar rashin kulawa da gyaran jiki wani namiji ba zai iya bude baki ya fada ba.

Koda ita matar ma ba zai iya fada mata ba sai dai kurum ka ga ana rigima ita tana ta ganin yana yi mata wulakanci shi kuma ga abin da yake gani daban, don haka yana da matukar muhimmancin ga ma’aurata da su himmantu wajen gyara jiki ba su kadai ba, har da wanda ba su yi aure ba domin addinin musulunci ma ya zo mana da nuni na kulawa da tsafta.

Sirrin Mace

Kowacce mace ta san cewa sirri ne a tare da ita sutura al’aurarta musamman ma ga mace mai aure

Yana daga cikin sutura al’aurarta da kula da gyaranta domin ita ce babbar hanya da idan ba kya kulawa da gyara ta hakika za ki fuskanci illolo daban-daban kamar za ki ji haka kawai kina wari.

Maigida zai rika gudunki, za ki ga kina fitar da ruwa mai kazanta a yayin al’ada kuma doyi ma za ki rika yi don ko dakinki aka shiga za a ji yana ta doyi.

To amma idan kina kula da tsafta hakika duka wannan za ki ji kin rabu da shi, kuma maigida ba zai rika baya-baya da ke ba, bare har ta kai ga rabuwar aure.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Nijar : Kasashen Faransa da Amurka ne ke kitsa mana hare-haren ta’addanci  

Shugaban Nijar Janar Abdourahmane Tiani ya ce har yanzu ana wa kasarsa zagon kasa ta fuskar tsaro musamman daga kasashen yamma.

Janar Tiani ya ambato kasar Faransa da tsohuwar gwamnatin Amurka a matsayin wadanda ke da hannu a matsalolin tsaro da ake fama da su.

Ya bayyana hakan ne a wata hira ta musamman da gidan talabijin na kasar RTN da aka watsa a yammacin ranar Asabar.

Ya dai yi bayyani ne kan batutuwa daban daban ciki har da halin da kasar ke ciki.

Shugaban kasar ta Nijar, ya kuma jinjinawa sojojin kasar dake bakin daga domin tsare kasar dare da rana, ya kuma isar da ta’aziyya ga sojojin da suka rasa rayukansu a kokarin kare kasar daga sha’anin ta’addanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uba ya harbe ɗansa har lahira saboda zaton biri ne
  • Uba ya harbe ɗansa bisa saboda zaton biri ne
  • Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 
  • Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo
  • Nijar : Kasashen Faransa da Amurka ne ke kitsa mana hare-haren ta’addanci  
  • Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici
  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)
  • Sojoji sun cafke ɗan ta’adda sun ƙwato makamai a Filato
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Iran Na Rashin Tunanin Kera Makamin Nukiliya